< yihūdāḥ 1 >

1 yīśukhrīṣṭasya dāso yākūbo bhrātā yihūdāstāteneśvareṇa pavitrīkṛtān yīśukhrīṣṭena rakṣitāṁścāhūtān lokān prati patraṁ likhati|
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 kṛpā śāntiḥ prema ca bāhulyarūpeṇa yuṣmāsvadhitiṣṭhatu|
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 he priyāḥ, sādhāraṇaparitrāṇamadhi yuṣmān prati lekhituṁ mama bahuyatne jāte pūrvvakāle pavitralokeṣu samarpito yo dharmmastadarthaṁ yūyaṁ prāṇavyayenāpi saceṣṭā bhavateti vinayārthaṁ yuṣmān prati patralekhanamāvaśyakam amanye|
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 yasmād etadrūpadaṇḍaprāptaye pūrvvaṁ likhitāḥ kecijjanā asmān upasṛptavantaḥ, te 'dhārmmikalokā asmākam īśvarasyānugrahaṁ dhvajīkṛtya lampaṭatām ācaranti, advitīyo 'dhipati ryo 'smākaṁ prabhu ryīśukhrīṣṭastaṁ nāṅgīkurvvanti|
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 tasmād yūyaṁ purā yad avagatāstat puna ryuṣmān smārayitum icchāmi, phalataḥ prabhurekakṛtvaḥ svaprajā misaradeśād udadhāra yat tataḥ param aviśvāsino vyanāśayat|
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 ye ca svargadūtāḥ svīyakartṛtvapade na sthitvā svavāsasthānaṁ parityaktavantastān sa mahādinasya vicārārtham andhakāramaye 'dhaḥsthāne sadāsthāyibhi rbandhanairabadhnāt| (aïdios g126)
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
7 aparaṁ sidomam amorā tannikaṭasthanagarāṇi caiteṣāṁ nivāsinastatsamarūpaṁ vyabhicāraṁ kṛtavanto viṣamamaithunasya ceṣṭayā vipathaṁ gatavantaśca tasmāt tānyapi dṛṣṭāntasvarūpāṇi bhūtvā sadātanavahninā daṇḍaṁ bhuñjate| (aiōnios g166)
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
8 tathaiveme svapnācāriṇo'pi svaśarīrāṇi kalaṅkayanti rājādhīnatāṁ na svīkurvvantyuccapadasthān nindanti ca|
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 kintu pradhānadivyadūto mīkhāyelo yadā mūsaso dehe śayatānena vivadamānaḥ samabhāṣata tadā tisman nindārūpaṁ daṇḍaṁ samarpayituṁ sāhasaṁ na kṛtvākathayat prabhustvāṁ bhartsayatāṁ|
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 kintvime yanna budhyante tannindanti yacca nirbbodhapaśava ivendriyairavagacchanti tena naśyanti|
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 tān dhik, te kābilo mārge caranti pāritoṣikasyāśāto biliyamo bhrāntimanudhāvanti korahasya durmmukhatvena vinaśyanti ca|
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 yuṣmākaṁ premabhojyeṣu te vighnajanakā bhavanti, ātmambharayaśca bhūtvā nirlajjayā yuṣmābhiḥ sārddhaṁ bhuñjate| te vāyubhiścālitā nistoyameghā hemantakālikā niṣphalā dvi rmṛtā unmūlitā vṛkṣāḥ,
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 svakīyalajjāpheṇodvamakāḥ pracaṇḍāḥ sāmudrataraṅgāḥ sadākālaṁ yāvat ghoratimirabhāgīni bhramaṇakārīṇi nakṣatrāṇi ca bhavanti| (aiōn g165)
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
14 ādamataḥ saptamaḥ puruṣo yo hanokaḥ sa tānuddiśya bhaviṣyadvākyamidaṁ kathitavān, yathā, paśya svakīyapuṇyānām ayutai rveṣṭitaḥ prabhuḥ|
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 sarvvān prati vicārājñāsādhanāyāgamiṣyati| tadā cādhārmmikāḥ sarvve jātā yairaparādhinaḥ| vidharmmakarmmaṇāṁ teṣāṁ sarvveṣāmeva kāraṇāt| tathā tadvaiparītyenāpyadharmmācāripāpināṁ| uktakaṭhoravākyānāṁ sarvveṣāmapi kāraṇāt| parameśena doṣitvaṁ teṣāṁ prakāśayiṣyate||
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 te vākkalahakāriṇaḥ svabhāgyanindakāḥ svecchācāriṇo darpavādimukhaviśiṣṭā lābhārthaṁ manuṣyastāvakāśca santi|
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 kintu he priyatamāḥ, asmākaṁ prabho ryīśukhrīṣṭasya preritai ryad vākyaṁ pūrvvaṁ yuṣmabhyaṁ kathitaṁ tat smarata,
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 phalataḥ śeṣasamaye svecchāto 'dharmmācāriṇo nindakā upasthāsyantīti|
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 ete lokāḥ svān pṛthak kurvvantaḥ sāṁsārikā ātmahīnāśca santi|
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 kintu he priyatamāḥ, yūyaṁ sveṣām atipavitraviśvāse nicīyamānāḥ pavitreṇātmanā prārthanāṁ kurvvanta
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 īśvarasya premnā svān rakṣata, anantajīvanāya cāsmākaṁ prabho ryīśukhrīṣṭasya kṛpāṁ pratīkṣadhvaṁ| (aiōnios g166)
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
22 aparaṁ yūyaṁ vivicya kāṁścid anukampadhvaṁ
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 kāṁścid agnita uddhṛtya bhayaṁ pradarśya rakṣata, śārīrikabhāvena kalaṅkitaṁ vastramapi ṛtīyadhvaṁ|
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 aparañca yuṣmān skhalanād rakṣitum ullāsena svīyatejasaḥ sākṣāt nirddoṣān sthāpayituñca samartho
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 yo 'smākam advitīyastrāṇakarttā sarvvajña īśvarastasya gauravaṁ mahimā parākramaḥ kartṛtvañcedānīm anantakālaṁ yāvad bhūyāt| āmen| (aiōn g165)
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)

< yihūdāḥ 1 >