< yohanaḥ 7 >

1 tataḥ paraṁ yihūdīyalokāstaṁ hantuṁ samaihanta tasmād yīśu ryihūdāpradeśe paryyaṭituṁ necchan gālīl pradeśe paryyaṭituṁ prārabhata|
Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
2 kintu tasmin samaye yihūdīyānāṁ dūṣyavāsanāmotsava upasthite
Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
3 tasya bhrātarastam avadan yāni karmmāṇi tvayā kriyante tāni yathā tava śiṣyāḥ paśyanti tadarthaṁ tvamitaḥ sthānād yihūdīyadeśaṁ vraja|
sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
4 yaḥ kaścit svayaṁ pracikāśiṣati sa kadāpi guptaṁ karmma na karoti yadīdṛśaṁ karmma karoṣi tarhi jagati nijaṁ paricāyaya|
Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
5 yatastasya bhrātaropi taṁ na viśvasanti|
Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
6 tadā yīśustān avocat mama samaya idānīṁ nopatiṣṭhati kintu yuṣmākaṁ samayaḥ satatam upatiṣṭhati|
Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
7 jagato lokā yuṣmān ṛtīyituṁ na śakruvanti kintu māmeva ṛtīyante yatasteṣāṁ karmāṇi duṣṭāni tatra sākṣyamidam ahaṁ dadāmi|
Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
8 ataeva yūyam utsave'smin yāta nāham idānīm asminnutsave yāmi yato mama samaya idānīṁ na sampūrṇaḥ|
Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
9 iti vākyam ukttvā sa gālīli sthitavān
Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
10 kintu tasya bhrātṛṣu tatra prasthiteṣu satsu so'prakaṭa utsavam agacchat|
Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
11 anantaram utsavam upasthitā yihūdīyāstaṁ mṛgayitvāpṛcchan sa kutra?
A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
12 tato lokānāṁ madhye tasmin nānāvidhā vivādā bhavitum ārabdhavantaḥ| kecid avocan sa uttamaḥ puruṣaḥ kecid avocan na tathā varaṁ lokānāṁ bhramaṁ janayati|
A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
13 kintu yihūdīyānāṁ bhayāt kopi tasya pakṣe spaṣṭaṁ nākathayat|
Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
14 tataḥ param utsavasya madhyasamaye yīśu rmandiraṁ gatvā samupadiśati sma|
Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
15 tato yihūdīyā lokā āścaryyaṁ jñātvākathayan eṣā mānuṣo nādhītyā katham etādṛśo vidvānabhūt?
Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
16 tadā yīśuḥ pratyavocad upadeśoyaṁ na mama kintu yo māṁ preṣitavān tasya|
Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
17 yo jano nideśaṁ tasya grahīṣyati mamopadeśo matto bhavati kim īśvarād bhavati sa ganastajjñātuṁ śakṣyati|
Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
18 yo janaḥ svataḥ kathayati sa svīyaṁ gauravam īhate kintu yaḥ prerayitu rgauravam īhate sa satyavādī tasmin kopyadharmmo nāsti|
Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
19 mūsā yuṣmabhyaṁ vyavasthāgranthaṁ kiṁ nādadāt? kintu yuṣmākaṁ kopi tāṁ vyavasthāṁ na samācarati| māṁ hantuṁ kuto yatadhve?
Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
20 tadā lokā avadan tvaṁ bhūtagrastastvāṁ hantuṁ ko yatate?
Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
21 tato yīśuravocad ekaṁ karmma mayākāri tasmād yūyaṁ sarvva mahāścaryyaṁ manyadhve|
Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
22 mūsā yuṣmabhyaṁ tvakchedavidhiṁ pradadau sa mūsāto na jātaḥ kintu pitṛpuruṣebhyo jātaḥ tena viśrāmavāre'pi mānuṣāṇāṁ tvakchedaṁ kurutha|
Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
23 ataeva viśrāmavāre manuṣyāṇāṁ tvakchede kṛte yadi mūsāvyavasthāmaṅganaṁ na bhavati tarhi mayā viśrāmavāre mānuṣaḥ sampūrṇarūpeṇa svastho'kāri tatkāraṇād yūyaṁ kiṁ mahyaṁ kupyatha?
To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
24 sapakṣapātaṁ vicāramakṛtvā nyāyyaṁ vicāraṁ kuruta|
Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
25 tadā yirūśālam nivāsinaḥ katipayajanā akathayan ime yaṁ hantuṁ ceṣṭante sa evāyaṁ kiṁ na?
A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
26 kintu paśyata nirbhayaḥ san kathāṁ kathayati tathāpi kimapi a vadantyete ayamevābhiṣiktto bhavatīti niścitaṁ kimadhipatayo jānanti?
Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
27 manujoyaṁ kasmādāgamad iti vayaṁ jānomaḥ kintvabhiṣiktta āgate sa kasmādāgatavān iti kopi jñātuṁ na śakṣyati|
Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
28 tadā yīśu rmadhyemandiram upadiśan uccaiḥkāram ukttavān yūyaṁ kiṁ māṁ jānītha? kasmāccāgatosmi tadapi kiṁ jānītha? nāhaṁ svata āgatosmi kintu yaḥ satyavādī saeva māṁ preṣitavān yūyaṁ taṁ na jānītha|
Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
29 tamahaṁ jāne tenāhaṁ prerita agatosmi|
amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
30 tasmād yihūdīyāstaṁ dharttum udyatāstathāpi kopi tasya gātre hastaṁ nārpayad yato hetostadā tasya samayo nopatiṣṭhati|
Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
31 kintu bahavo lokāstasmin viśvasya kathitavānto'bhiṣikttapuruṣa āgatya mānuṣasyāsya kriyābhyaḥ kim adhikā āścaryyāḥ kriyāḥ kariṣyati?
Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
32 tataḥ paraṁ lokāstasmin itthaṁ vivadante phirūśinaḥ pradhānayājakāñceti śrutavantastaṁ dhṛtvā netuṁ padātigaṇaṁ preṣayāmāsuḥ|
Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
33 tato yīśuravadad aham alpadināni yuṣmābhiḥ sārddhaṁ sthitvā matprerayituḥ samīpaṁ yāsyāmi|
Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
34 māṁ mṛgayiṣyadhve kintūddeśaṁ na lapsyadhve ratra sthāsyāmi tatra yūyaṁ gantuṁ na śakṣyatha|
Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
35 tadā yihūdīyāḥ parasparaṁ vakttumārebhire asyoddeśaṁ na prāpsyāma etādṛśaṁ kiṁ sthānaṁ yāsyati? bhinnadeśe vikīrṇānāṁ yihūdīyānāṁ sannidhim eṣa gatvā tān upadekṣyati kiṁ?
Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
36 no cet māṁ gaveṣayiṣyatha kintūddeśaṁ na prāpsyatha eṣa kodṛśaṁ vākyamidaṁ vadati?
Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
37 anantaram utsavasya carame'hani arthāt pradhānadine yīśuruttiṣṭhan uccaiḥkāram āhvayan uditavān yadi kaścit tṛṣārtto bhavati tarhi mamāntikam āgatya pivatu|
A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
38 yaḥ kaścinmayi viśvasiti dharmmagranthasya vacanānusāreṇa tasyābhyantarato'mṛtatoyasya srotāṁsi nirgamiṣyanti|
Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
39 ye tasmin viśvasanti ta ātmānaṁ prāpsyantītyarthe sa idaṁ vākyaṁ vyāhṛtavān etatkālaṁ yāvad yīśu rvibhavaṁ na prāptastasmāt pavitra ātmā nādīyata|
Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
40 etāṁ vāṇīṁ śrutvā bahavo lokā avadan ayameva niścitaṁ sa bhaviṣyadvādī|
Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
41 kecid akathayan eṣaeva sobhiṣikttaḥ kintu kecid avadan sobhiṣikttaḥ kiṁ gālīl pradeśe janiṣyate?
Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
42 sobhiṣiktto dāyūdo vaṁśe dāyūdo janmasthāne baitlehami pattane janiṣyate dharmmagranthe kimitthaṁ likhitaṁ nāsti?
Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
43 itthaṁ tasmin lokānāṁ bhinnavākyatā jātā|
Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
44 katipayalokāstaṁ dharttum aicchan tathāpi tadvapuṣi kopi hastaṁ nārpayat|
Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
45 anantaraṁ pādātigaṇe pradhānayājakānāṁ phirūśināñca samīpamāgatavati te tān apṛcchan kuto hetostaṁ nānayata?
A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
46 tadā padātayaḥ pratyavadan sa mānava iva kopi kadāpi nopādiśat|
Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
47 tataḥ phirūśinaḥ prāvocan yūyamapi kimabhrāmiṣṭa?
Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
48 adhipatīnāṁ phirūśināñca kopi kiṁ tasmin vyaśvasīt?
Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
49 ye śāstraṁ na jānanti ta ime'dhamalokāeva śāpagrastāḥ|
A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
50 tadā nikadīmanāmā teṣāmeko yaḥ kṣaṇadāyāṁ yīśoḥ sannidhim agāt sa ukttavān
Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
51 tasya vākye na śrute karmmaṇi ca na vidite 'smākaṁ vyavasthā kiṁ kañcana manujaṁ doṣīkaroti?
“Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
52 tataste vyāharan tvamapi kiṁ gālīlīyalokaḥ? vivicya paśya galīli kopi bhaviṣyadvādī notpadyate|
Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
53 tataḥ paraṁ sarvve svaṁ svaṁ gṛhaṁ gatāḥ kintu yīśu rjaitunanāmānaṁ śiloccayaṁ gatavān|
Sai kowannensu ya koma gidansa.

< yohanaḥ 7 >