< preritāḥ 6 >
1 tasmin samaye śiṣyāṇāṁ bāhulyāt prātyahikadānasya viśrāṇanai rbhinnadeśīyānāṁ vidhavāstrīgaṇa upekṣite sati ibrīyalokaiḥ sahānyadeśīyānāṁ vivāda upātiṣṭhat|
A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum.
2 tadā dvādaśapreritāḥ sarvvān śiṣyān saṁgṛhyākathayan īśvarasya kathāpracāraṁ parityajya bhojanagaveṣaṇam asmākam ucitaṁ nahi|
Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba.
3 ato he bhrātṛgaṇa vayam etatkarmmaṇo bhāraṁ yebhyo dātuṁ śaknuma etādṛśān sukhyātyāpannān pavitreṇātmanā jñānena ca pūrṇān sapprajanān yūyaṁ sveṣāṁ madhye manonītān kuruta,
’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki
4 kintu vayaṁ prārthanāyāṁ kathāpracārakarmmaṇi ca nityapravṛttāḥ sthāsyāmaḥ|
mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”
5 etasyāṁ kathāyāṁ sarvve lokāḥ santuṣṭāḥ santaḥ sveṣāṁ madhyāt stiphānaḥ philipaḥ prakharo nikānor tīman parmmiṇā yihūdimatagrāhī-āntiyakhiyānagarīyo nikalā etān paramabhaktān pavitreṇātmanā paripūrṇān sapta janān
Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci.
6 preritānāṁ samakṣam ānayan, tataste prārthanāṁ kṛtvā teṣāṁ śiraḥsu hastān ārpayan|
Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.
7 aparañca īśvarasya kathā deśaṁ vyāpnot viśeṣato yirūśālami nagare śiṣyāṇāṁ saṁkhyā prabhūtarūpeṇāvarddhata yājakānāṁ madhyepi bahavaḥ khrīṣṭamatagrāhiṇo'bhavan|
Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.
8 stiphāno viśvāsena parākrameṇa ca paripūrṇaḥ san lokānāṁ madhye bahuvidham adbhutam āścaryyaṁ karmmākarot|
To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane.
9 tena libarttinīyanāmnā vikhyātasaṅghasya katipayajanāḥ kurīṇīyasikandarīya-kilikīyāśīyādeśīyāḥ kiyanto janāścotthāya stiphānena sārddhaṁ vyavadanta|
Sai hamayya ta taso daga’yan ƙungiyar Majami’a na’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
10 kintu stiphāno jñānena pavitreṇātmanā ca īdṛśīṁ kathāṁ kathitavān yasyāste āpattiṁ karttuṁ nāśaknuvan|
amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.
11 paścāt tai rlobhitāḥ katipayajanāḥ kathāmenām akathayan, vayaṁ tasya mukhato mūsā īśvarasya ca nindāvākyam aśrauṣma|
Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”
12 te lokānāṁ lokaprācīnānām adhyāpakānāñca pravṛttiṁ janayitvā stiphānasya sannidhim āgatya taṁ dhṛtvā mahāsabhāmadhyam ānayan|
Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa.
13 tadanantaraṁ katipayajaneṣu mithyāsākṣiṣu samānīteṣu te'kathayan eṣa jana etatpuṇyasthānavyavasthayo rnindātaḥ kadāpi na nivarttate|
Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka.
14 phalato nāsaratīyayīśuḥ sthānametad ucchinnaṁ kariṣyati mūsāsamarpitam asmākaṁ vyavaharaṇam anyarūpaṁ kariṣyati tasyaitādṛśīṁ kathāṁ vayam aśṛṇuma|
Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”
15 tadā mahāsabhāsthāḥ sarvve taṁ prati sthirāṁ dṛṣṭiṁ kṛtvā svargadūtamukhasadṛśaṁ tasya mukham apaśyan|
Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.