< 2 karinthinaḥ 12 >

1 ātmaślāghā mamānupayuktā kintvahaṁ prabho rdarśanādeśānām ākhyānaṁ kathayituṁ pravartte|
Dole in ci gaba da yin taƙama. Ko da yake ba za tă amfane ni ba, zan yi magana a kan ru’uyoyi da wahayoyi waɗanda na karɓa daga Ubangiji.
2 itaścaturdaśavatsarebhyaḥ pūrvvaṁ mayā paricita eko janastṛtīyaṁ svargamanīyata, sa saśarīreṇa niḥśarīreṇa vā tat sthānamanīyata tadahaṁ na jānāmi kintvīśvaro jānāti|
Na san wani a cikin Kiristi wanda shekaru goma sha huɗu da suka wuce an ɗauke zuwa sama ta uku. Ko a cikin jiki ne, ko kuwa ba a cikin jiki ba, ni dai ban sani ba, Allah ne ya sani.
3 sa mānavaḥ svargaṁ nītaḥ san akathyāni marttyavāgatītāni ca vākyāni śrutavān|
Na kuma san cewa wannan mutum, ko a cikin jiki ne, ko kuma ba a cikin jiki ba, ni dai ban sani ba, amma Allah ne ya sani,
4 kintu tadānīṁ sa saśarīro niḥśarīro vāsīt tanmayā na jñāyate tad īśvareṇaiva jñāyate|
an ɗauke shi ne zuwa aljanna. Ya ji waɗansu abubuwa waɗanda ba zai iya faɗarsu da kalmomi ba, abubuwan da ba a ba wa mutum damar faɗi.
5 tamadhyahaṁ ślāghiṣye māmadhi nānyena kenacid viṣayeṇa ślāghiṣye kevalaṁ svadaurbbalyena ślāghiṣye|
Zan yi taƙama game da mutum irin wannan, sai dai ni ba zan yi taƙama da kaina ba, sai dai a kan rashin ƙarfina.
6 yadyaham ātmaślāghāṁ karttum iccheyaṁ tathāpi nirbbodha iva na bhaviṣyāmi yataḥ satyameva kathayiṣyāmi, kintu lokā māṁ yādṛśaṁ paśyanti mama vākyaṁ śrutvā vā yādṛśaṁ māṁ manyate tasmāt śreṣṭhaṁ māṁ yanna gaṇayanti tadarthamahaṁ tato viraṁsyāmi|
Ko da zan so yin gadara ma, ba zan zama wawa ba, gama gaskiya zan faɗa. Amma na bar zancen haka, don kada wani ya ɗauke ni fiye da yadda yake ganina, ko yadda yake jin maganata.
7 aparam utkṛṣṭadarśanaprāptito yadaham ātmābhimānī na bhavāmi tadarthaṁ śarīravedhakam ekaṁ śūlaṁ mahyam adāyi tat madīyātmābhimānanivāraṇārthaṁ mama tāḍayitā śayatāno dūtaḥ|
Don kada in cika da girman kai saboda waɗannan mafifitan manyan wahayoyi, sai aka sa mini wata ƙaya a jikina wadda ta zama ɗan saƙon Shaiɗan, don ta wahalshe ni.
8 mattastasya prasthānaṁ yācitumahaṁ tristamadhi prabhumuddiśya prārthanāṁ kṛtavān|
Sau uku na roƙi Ubangiji yă raba ni da wannan abu.
9 tataḥ sa māmuktavān mamānugrahastava sarvvasādhakaḥ, yato daurbbalyāt mama śaktiḥ pūrṇatāṁ gacchatīti| ataḥ khrīṣṭasya śakti ryanmām āśrayati tadarthaṁ svadaurbbalyena mama ślāghanaṁ sukhadaṁ|
Amma ya ce mini, “Alherina ya ishe ka, domin a cikin rashin ƙarfi ne ake ganin cikar ikona.” Saboda haka, zan ƙara yin taƙama da farin ciki game da rashin ƙarfina, domin ikon Yesu Kiristi yă zauna tare da ni.
10 tasmāt khrīṣṭaheto rdaurbbalyanindādaridratāvipakṣatākaṣṭādiṣu santuṣyāmyahaṁ| yadāhaṁ durbbalo'smi tadaiva sabalo bhavāmi|
Shi ya sa nake murna cikin rashin ƙarfi, da zagi, da shan wahaloli, da tsanantawa, da matsaloli, saboda Kiristi. Don a sa’ad da nake marar ƙarfi a nan ne nake da ƙarfi.
11 etenātmaślāghanenāhaṁ nirbbodha ivābhavaṁ kintu yūyaṁ tasya kāraṇaṁ yato mama praśaṁsā yuṣmābhireva karttavyāsīt| yadyapyam agaṇyo bhaveyaṁ tathāpi mukhyatamebhyaḥ preritebhyaḥ kenāpi prakāreṇa nāhaṁ nyūno'smi|
Na yi wauta kam, amma ku ne kuke tilasta mini, ku ne kuwa ya kamata ku yaba mini, domin ba inda na kāsa waɗannan mafiffitan manzanni, ko da yake ni ba kome ba ne.
12 sarvvathādbhutakriyāśaktilakṣaṇaiḥ preritasya cihnāni yuṣmākaṁ madhye sadhairyyaṁ mayā prakāśitāni|
Abubuwan da suke tabbatar da manzo, alamu, abubuwa da kuma ayyukan banmamaki, an aikata su a cikinku da matuƙar nacewa.
13 mama pālanārthaṁ yūyaṁ mayā bhārākrāntā nābhavataitad ekaṁ nyūnatvaṁ vināparābhyaḥ samitibhyo yuṣmākaṁ kiṁ nyūnatvaṁ jātaṁ? anena mama doṣaṁ kṣamadhvaṁ|
Ta yaya ne darajarku ba tă kai ta sauran ikkilisiyoyi ba, ko kuwa don dai ban nawaita muku ba ne? Ku gafarta mini wannan laifi!
14 paśyata tṛtīyavāraṁ yuṣmatsamīpaṁ gantumudyato'smi tatrāpyahaṁ yuṣmān bhārākrāntān na kariṣyāmi| yuṣmākaṁ sampattimahaṁ na mṛgaye kintu yuṣmāneva, yataḥ pitroḥ kṛte santānānāṁ dhanasañcayo'nupayuktaḥ kintu santānānāṁ kṛte pitro rdhanasañcaya upayuktaḥ|
Yanzu a shirye nake in ziyarce ku sau na uku, ba zan kuma nawaita muku ba, don ba kayanku nake so ba, ku nake so. Gama ba yara ne da ɗaukar nauyin iyayensu ba, sai dai iyaye ne da ɗaukar nauyin yaran.
15 aparañca yuṣmāsu bahu prīyamāṇo'pyahaṁ yadi yuṣmatto'lpaṁ prama labhe tathāpi yuṣmākaṁ prāṇarakṣārthaṁ sānandaṁ bahu vyayaṁ sarvvavyayañca kariṣyāmi|
Don haka ina farin ciki in kashe dukan abin da nake da shi a kanku, har in ba da kaina ma dominku. In na ƙaunace ku fiye da haka, za ku rage ƙaunarku gare ni ne?
16 yūyaṁ mayā kiñcidapi na bhārākrāntā iti satyaṁ, kintvahaṁ dhūrttaḥ san chalena yuṣmān vañcitavān etat kiṁ kenacid vaktavyaṁ?
To, shi ke nan, ban nawaita muku ba. Ashe, sai ku ce dabara na yi muku, na shawo kanku ta hanyar yaudara!
17 yuṣmatsamīpaṁ mayā ye lokāḥ prahitāsteṣāmekena kiṁ mama ko'pyarthalābho jātaḥ?
Na cuce ku ne ta wurin wani daga cikin waɗanda na aiko a gare ku?
18 ahaṁ tītaṁ vinīya tena sārddhaṁ bhrātaramekaṁ preṣitavān yuṣmattastītena kim artho labdhaḥ? ekasmin bhāva ekasya padacihneṣu cāvāṁ kiṁ na caritavantau?
Na roƙi Titus ya zo wurinku. Na kuma aiki ɗan’uwanmu tare da shi. Ko Titus ya cuce ku ne? Ba ruhu ɗaya yake bi da mu ba? Ba kuma hanya guda muka bi ba?
19 yuṣmākaṁ samīpe vayaṁ puna rdoṣakṣālanakathāṁ kathayāma iti kiṁ budhyadhve? he priyatamāḥ, yuṣmākaṁ niṣṭhārthaṁ vayamīśvarasya samakṣaṁ khrīṣṭena sarvvāṇyetāni kathayāmaḥ|
Ko tun dā can, kuna tsammani muna kāre kanmu a gare ku ne? A gaban Allah muke magana, kamar waɗanda suke cikin Kiristi. Ƙaunatattuna, kome da muke yi, muna yi ne don inganta ku ne.
20 ahaṁ yadāgamiṣyāmi, tadā yuṣmān yādṛśān draṣṭuṁ necchāmi tādṛśān drakṣyāmi, yūyamapi māṁ yādṛśaṁ draṣṭuṁ necchatha tādṛśaṁ drakṣyatha, yuṣmanmadhye vivāda īrṣyā krodho vipakṣatā parāpavādaḥ karṇejapanaṁ darpaḥ kalahaścaite bhaviṣyanti;
Gama ina tsoro, in na zo, in tarar da ku dabam da yadda nake so, ku ma ku tarar da ni dabam da yadda kuke so. Ina tsoro kada yă zama akwai faɗa, da kishi, da fushi mai zafi, da tsattsaguwa, da ɓata suna, da gulma, da girman kai, da hargitsi.
21 tenāhaṁ yuṣmatsamīpaṁ punarāgatya madīyeśvareṇa namayiṣye, pūrvvaṁ kṛtapāpān lokān svīyāśucitāveśyāgamanalampaṭatācaraṇād anutāpam akṛtavanto dṛṣṭvā ca tānadhi mama śoko janiṣyata iti bibhemi|
Ina tsoro kada sa’ad da na sāke zuwa, Allahna zai ƙasƙantar da ni a gabanku, kuma in yi baƙin ciki saboda waɗanda suka yi zunubi a dā, ba su kuma tuba daga aikin ƙazanta, da na fasikanci, da kuma lalata da suka sa kansu a ciki ba.

< 2 karinthinaḥ 12 >