< mathiH 4 >
1 tataH paraM yIzuH pratArakENa parIkSitO bhavitum AtmanA prAntaram AkRSTaH
Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi.
2 san catvAriMzadahOrAtrAn anAhArastiSThan kSudhitO babhUva|
Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa.
3 tadAnIM parIkSitA tatsamIpam Agatya vyAhRtavAn, yadi tvamIzvarAtmajO bhavEstarhyAjnjayA pASANAnEtAn pUpAn vidhEhi|
Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”
4 tataH sa pratyabravIt, itthaM likhitamAstE, "manujaH kEvalapUpEna na jIviSyati, kintvIzvarasya vadanAd yAni yAni vacAMsi niHsaranti tairEva jIviSyati|"
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’”
5 tadA pratArakastaM puNyanagaraM nItvA mandirasya cUPOpari nidhAya gaditavAn,
Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali.
6 tvaM yadizvarasya tanayO bhavEstarhItO'dhaH pata, yata itthaM likhitamAstE, AdEkSyati nijAn dUtAn rakSituM tvAM paramEzvaraH| yathA sarvvESu mArgESu tvadIyacaraNadvayE| na lagEt prastarAghAtastvAM ghariSyanti tE karaiH||
Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
7 tadAnIM yIzustasmai kathitavAn Etadapi likhitamAstE, "tvaM nijaprabhuM paramEzvaraM mA parIkSasva|"
Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
8 anantaraM pratArakaH punarapi tam atyunjcadharAdharOpari nItvA jagataH sakalarAjyAni tadaizvaryyANi ca darzayAzcakAra kathayAnjcakAra ca,
Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
9 yadi tvaM daNPavad bhavan mAM praNamEstarhyaham EtAni tubhyaM pradAsyAmi|
Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”
10 tadAnIM yIzustamavOcat, dUrIbhava pratAraka, likhitamidam AstE, "tvayA nijaH prabhuH paramEzvaraH praNamyaH kEvalaH sa sEvyazca|"
Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’”
11 tataH pratArakENa sa paryyatyAji, tadA svargIyadUtairAgatya sa siSEvE|
Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.
12 tadanantaraM yOhan kArAyAM babandhE, tadvArttAM nizamya yIzunA gAlIl prAsthIyata|
Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili.
13 tataH paraM sa nAsarannagaraM vihAya jalaghEstaTE sibUlUnnaptAlI EtayOruvabhayOH pradEzayOH sImnOrmadhyavarttI ya: kapharnAhUm tannagaram itvA nyavasat|
Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali
14 tasmAt, anyAdEzIyagAlIli yarddanpArE'bdhirOdhasi| naptAlisibUlUndEzau yatra sthAnE sthitau purA|
don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,
15 tatratyA manujA yE yE paryyabhrAmyan tamisrakE| tairjanairbRhadAlOkaH paridarziSyatE tadA| avasan yE janA dEzE mRtyucchAyAsvarUpakE| tESAmupari lOkAnAmAlOkaH saMprakAzitaH||
“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun, wannan yankin Galili ta Al’ummai,
16 yadEtadvacanaM yizayiyabhaviSyadvAdinA prOktaM, tat tadA saphalam abhUt|
mutanen da suke zama cikin duhu sun ga babban haske; haske kuma ya haskaka a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”
17 anantaraM yIzuH susaMvAdaM pracArayan EtAM kathAM kathayitum ArEbhE, manAMsi parAvarttayata, svargIyarAjatvaM savidhamabhavat|
Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
18 tataH paraM yIzu rgAlIlO jaladhEstaTEna gacchan gacchan Andriyastasya bhrAtA zimOn arthatO yaM pitaraM vadanti EtAvubhau jalaghau jAlaM kSipantau dadarza, yatastau mInadhAriNAvAstAm|
Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne.
19 tadA sa tAvAhUya vyAjahAra, yuvAM mama pazcAd AgacchataM, yuvAmahaM manujadhAriNau kariSyAmi|
Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.”
20 tEnaiva tau jAlaM vihAya tasya pazcAt AgacchatAm|
Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.
21 anantaraM tasmAt sthAnAt vrajan vrajan sivadiyasya sutau yAkUb yOhannAmAnau dvau sahajau tAtEna sArddhaM naukOpari jAlasya jIrNOddhAraM kurvvantau vIkSya tAvAhUtavAn|
Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su,
22 tatkSaNAt tau nAvaM svatAtanjca vihAya tasya pazcAdgAminau babhUvatuH|
nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.
23 anantaraM bhajanabhavanE samupadizan rAjyasya susaMvAdaM pracArayan manujAnAM sarvvaprakArAn rOgAn sarvvaprakArapIPAzca zamayan yIzuH kRtsnaM gAlIldEzaM bhramitum Arabhata|
Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane.
24 tEna kRtsnasuriyAdEzasya madhyaM tasya yazO vyApnOt, aparaM bhUtagrastA apasmArargINaH pakSAdhAtiprabhRtayazca yAvantO manujA nAnAvidhavyAdhibhiH kliSTA Asan, tESu sarvvESu tasya samIpam AnItESu sa tAn svasthAn cakAra|
Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.
25 EtEna gAlIl-dikApani-yirUzAlam-yihUdIyadEzEbhyO yarddanaH pArAnjca bahavO manujAstasya pazcAd Agacchan|
Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis, Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.