< lUkaH 19 >
1 yadA yIzu ryirIhOpuraM pravizya tanmadhyEna gacchaMstadA
Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
2 sakkEyanAmA karasanjcAyinAM pradhAnO dhanavAnEkO
Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
3 yIzuH kIdRgiti draSTuM cESTitavAn kintu kharvvatvAllOkasaMghamadhyE taddarzanamaprApya
Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
4 yEna pathA sa yAsyati tatpathE'grE dhAvitvA taM draSTum uPumbaratarumArurOha|
Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
5 pazcAd yIzustatsthAnam itvA UrddhvaM vilOkya taM dRSTvAvAdIt, hE sakkEya tvaM zIghramavarOha mayAdya tvadgEhE vastavyaM|
Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
6 tataH sa zIghramavaruhya sAhlAdaM taM jagrAha|
Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
7 tad dRSTvA sarvvE vivadamAnA vaktumArEbhirE, sOtithitvEna duSTalOkagRhaM gacchati|
Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
8 kintu sakkEyO daNPAyamAnO vaktumArEbhE, hE prabhO pazya mama yA sampattirasti tadarddhaM daridrEbhyO dadE, aparam anyAyaM kRtvA kasmAdapi yadi kadApi kinjcit mayA gRhItaM tarhi taccaturguNaM dadAmi|
Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
9 tadA yIzustamuktavAn ayamapi ibrAhImaH santAnO'taH kAraNAd adyAsya gRhE trANamupasthitaM|
Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
10 yad hAritaM tat mRgayituM rakSitunjca manuSyaputra AgatavAn|
Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
11 atha sa yirUzAlamaH samIpa upAtiSThad IzvararAjatvasyAnuSThAnaM tadaiva bhaviSyatIti lOkairanvabhUyata, tasmAt sa zrOtRbhyaH punardRSTAntakathAm utthApya kathayAmAsa|
Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
12 kOpi mahAllOkO nijArthaM rAjatvapadaM gRhItvA punarAgantuM dUradEzaM jagAma|
Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
13 yAtrAkAlE nijAn dazadAsAn AhUya dazasvarNamudrA dattvA mamAgamanaparyyantaM vANijyaM kurutEtyAdidEza|
Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
14 kintu tasya prajAstamavajnjAya manuSyamEnam asmAkamupari rAjatvaM na kArayivyAma imAM vArttAM tannikaTE prErayAmAsuH|
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
15 atha sa rAjatvapadaM prApyAgatavAn EkaikO janO bANijyEna kiM labdhavAn iti jnjAtuM yESu dAsESu mudrA arpayat tAn AhUyAnEtum AdidEza|
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
16 tadA prathama Agatya kathitavAn, hE prabhO tava tayaikayA mudrayA dazamudrA labdhAH|
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
17 tataH sa uvAca tvamuttamO dAsaH svalpEna vizvAsyO jAta itaH kAraNAt tvaM dazanagarANAm adhipO bhava|
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
18 dvitIya Agatya kathitavAn, hE prabhO tavaikayA mudrayA panjcamudrA labdhAH|
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
19 tataH sa uvAca, tvaM panjcAnAM nagarANAmadhipati rbhava|
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
20 tatOnya Agatya kathayAmAsa, hE prabhO pazya tava yA mudrA ahaM vastrE baddhvAsthApayaM sEyaM|
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
21 tvaM kRpaNO yannAsthApayastadapi gRhlAsi, yannAvapastadEva ca chinatsi tatOhaM tvattO bhItaH|
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
22 tadA sa jagAda, rE duSTadAsa tava vAkyEna tvAM dOSiNaM kariSyAmi, yadahaM nAsthApayaM tadEva gRhlAmi, yadahaM nAvapanjca tadEva chinadmi, EtAdRzaH kRpaNOhamiti yadi tvaM jAnAsi,
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
23 tarhi mama mudrA baNijAM nikaTE kutO nAsthApayaH? tayA kRtE'ham Agatya kusIdEna sArddhaM nijamudrA aprApsyam|
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
24 pazcAt sa samIpasthAn janAn AjnjApayat asmAt mudrA AnIya yasya dazamudrAH santi tasmai datta|
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
25 tE prOcuH prabhO'sya dazamudrAH santi|
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
26 yuSmAnahaM vadAmi yasyAzrayE vaddhatE 'dhikaM tasmai dAyiSyatE, kintu yasyAzrayE na varddhatE tasya yadyadasti tadapi tasmAn nAyiSyatE|
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
27 kintu mamAdhipatitvasya vazatvE sthAtum asammanyamAnA yE mama ripavastAnAnIya mama samakSaM saMharata|
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
28 ityupadEzakathAM kathayitvA sOgragaH san yirUzAlamapuraM yayau|
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
29 tatO baitphagIbaithanIyAgrAmayOH samIpE jaitunAdrErantikam itvA ziSyadvayam ityuktvA prESayAmAsa,
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
30 yuvAmamuM sammukhasthagrAmaM pravizyaiva yaM kOpi mAnuSaH kadApi nArOhat taM garddabhazAvakaM baddhaM drakSyathastaM mOcayitvAnayataM|
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
31 tatra kutO mOcayathaH? iti cEt kOpi vakSyati tarhi vakSyathaH prabhEratra prayOjanam AstE|
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
32 tadA tau praritau gatvA tatkathAnusArENa sarvvaM prAptau|
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
33 gardabhazAvakamOcanakAlE tatvAmina UcuH, gardabhazAvakaM kutO mOcayathaH?
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
34 tAvUcatuH prabhOratra prayOjanam AstE|
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
35 pazcAt tau taM gardabhazAvakaM yIzOrantikamAnIya tatpRSThE nijavasanAni pAtayitvA tadupari yIzumArOhayAmAsatuH|
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
36 atha yAtrAkAlE lOkAH pathi svavastrANi pAtayitum ArEbhirE|
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
37 aparaM jaitunAdrErupatyakAm itvA ziSyasaMghaH pUrvvadRSTAni mahAkarmmANi smRtvA,
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
38 yO rAjA prabhO rnAmnAyAti sa dhanyaH svargE kuzalaM sarvvOccE jayadhvani rbhavatu, kathAmEtAM kathayitvA sAnandam ucairIzvaraM dhanyaM vaktumArEbhE|
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
39 tadA lOkAraNyamadhyasthAH kiyantaH phirUzinastat zrutvA yIzuM prOcuH, hE upadEzaka svaziSyAn tarjaya|
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
40 sa uvAca, yuSmAnahaM vadAmi yadyamI nIravAstiSThanti tarhi pASANA ucaiH kathAH kathayiSyanti|
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
41 pazcAt tatpurAntikamEtya tadavalOkya sAzrupAtaM jagAda,
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
42 hA hA cEt tvamagrE'jnjAsyathAH, tavAsminnEva dinE vA yadi svamaggalam upAlapsyathAH, tarhyuttamam abhaviSyat, kintu kSaNEsmin tattava dRSTEragOcaram bhavati|
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
43 tvaM svatrANakAlE na manO nyadhatthA iti hEtO ryatkAlE tava ripavastvAM caturdikSu prAcIrENa vESTayitvA rOtsyanti
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
44 bAlakaiH sArddhaM bhUmisAt kariSyanti ca tvanmadhyE pASANaikOpi pASANOpari na sthAsyati ca, kAla IdRza upasthAsyati|
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
45 atha madhyEmandiraM pravizya tatratyAn krayivikrayiNO bahiSkurvvan
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
46 avadat madgRhaM prArthanAgRhamiti lipirAstE kintu yUyaM tadEva cairANAM gahvaraM kurutha|
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
47 pazcAt sa pratyahaM madhyEmandiram upadidEza; tataH pradhAnayAjakA adhyApakAH prAcInAzca taM nAzayituM cicESTirE;
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
48 kintu tadupadEzE sarvvE lOkA niviSTacittAH sthitAstasmAt tE tatkarttuM nAvakAzaM prApuH|
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.