< lUkaH 10 >
1 tataH paraM prabhuraparAn saptatiziSyAn niyujya svayaM yAni nagarANi yAni sthAnAni ca gamiSyati tAni nagarANi tAni sthAnAni ca prati dvau dvau janau prahitavAn|
Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
2 tEbhyaH kathayAmAsa ca zasyAni bahUnIti satyaM kintu chEdakA alpE; tasmAddhEtOH zasyakSEtrE chEdakAn aparAnapi prESayituM kSEtrasvAminaM prArthayadhvaM|
Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
3 yUyaM yAta, pazyata, vRkANAM madhyE mESazAvakAniva yuSmAn prahiNOmi|
Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
4 yUyaM kSudraM mahad vA vasanasampuTakaM pAdukAzca mA gRhlIta, mArgamadhyE kamapi mA namata ca|
Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
5 aparanjca yUyaM yad yat nivEzanaM pravizatha tatra nivEzanasyAsya maggalaM bhUyAditi vAkyaM prathamaM vadata|
“Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
6 tasmAt tasmin nivEzanE yadi maggalapAtraM sthAsyati tarhi tanmaggalaM tasya bhaviSyati, nOcEt yuSmAn prati parAvarttiSyatE|
In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
7 aparanjca tE yatkinjcid dAsyanti tadEva bhuktvA pItvA tasminnivEzanE sthAsyatha; yataH karmmakArI janO bhRtim arhati; gRhAd gRhaM mA yAsyatha|
Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
8 anyacca yuSmAsu kimapi nagaraM praviSTESu lOkA yadi yuSmAkam AtithyaM kariSyanti, tarhi yat khAdyam upasthAsyanti tadEva khAdiSyatha|
“Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
9 tannagarasthAn rOgiNaH svasthAn kariSyatha, IzvarIyaM rAjyaM yuSmAkam antikam Agamat kathAmEtAnjca pracArayiSyatha|
Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
10 kintu kimapi puraM yuSmAsu praviSTESu lOkA yadi yuSmAkam AtithyaM na kariSyanti, tarhi tasya nagarasya panthAnaM gatvA kathAmEtAM vadiSyatha,
Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
11 yuSmAkaM nagarIyA yA dhUlyO'smAsu samalagan tA api yuSmAkaM prAtikUlyEna sAkSyArthaM sampAtayAmaH; tathApIzvararAjyaM yuSmAkaM samIpam Agatam iti nizcitaM jAnIta|
‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
12 ahaM yuSmabhyaM yathArthaM kathayAmi, vicAradinE tasya nagarasya dazAtaH sidOmO dazA sahyA bhaviSyati|
Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
13 hA hA kOrAsIn nagara, hA hA baitsaidAnagara yuvayOrmadhyE yAdRzAni AzcaryyANi karmmANyakriyanta, tAni karmmANi yadi sOrasIdOnO rnagarayOrakAriSyanta, tadA itO bahudinapUrvvaM tannivAsinaH zaNavastrANi paridhAya gAtrESu bhasma vilipya samupavizya samakhEtsyanta|
“‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
14 atO vicAradivasE yuSmAkaM dazAtaH sOrasIdOnnivAsinAM dazA sahyA bhaviSyati|
A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
15 hE kapharnAhUm, tvaM svargaM yAvad unnatA kintu narakaM yAvat nyagbhaviSyasi| (Hadēs )
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
16 yO janO yuSmAkaM vAkyaM gRhlAti sa mamaiva vAkyaM gRhlAti; kinjca yO janO yuSmAkam avajnjAM karOti sa mamaivAvajnjAM karOti; yO janO mamAvajnjAM karOti ca sa matprErakasyaivAvajnjAM karOti|
“Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
17 atha tE saptatiziSyA AnandEna pratyAgatya kathayAmAsuH, hE prabhO bhavatO nAmnA bhUtA apyasmAkaM vazIbhavanti|
Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
18 tadAnIM sa tAn jagAda, vidyutamiva svargAt patantaM zaitAnam adarzam|
Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
19 pazyata sarpAn vRzcikAn ripOH sarvvaparAkramAMzca padatalai rdalayituM yuSmabhyaM zaktiM dadAmi tasmAd yuSmAkaM kApi hAni rna bhaviSyati|
Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
20 bhUtA yuSmAkaM vazIbhavanti, Etannimittat mA samullasata, svargE yuSmAkaM nAmAni likhitAni santIti nimittaM samullasata|
Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
21 tadghaTikAyAM yIzu rmanasi jAtAhlAdaH kathayAmAsa hE svargapRthivyOrEkAdhipatE pitastvaM jnjAnavatAM viduSAnjca lOkAnAM purastAt sarvvamEtad aprakAzya bAlakAnAM purastAt prAkAzaya EtasmAddhEtOstvAM dhanyaM vadAmi, hE pitaritthaM bhavatu yad EtadEva tava gOcara uttamam|
A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
22 pitrA sarvvANi mayi samarpitAni pitaraM vinA kOpi putraM na jAnAti kinjca putraM vinA yasmai janAya putrastaM prakAzitavAn tanjca vinA kOpi pitaraM na jAnAti|
“Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
23 tapaH paraM sa ziSyAn prati parAvRtya guptaM jagAda, yUyamEtAni sarvvANi pazyatha tatO yuSmAkaM cakSUMSi dhanyAni|
Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
24 yuSmAnahaM vadAmi, yUyaM yAni sarvvANi pazyatha tAni bahavO bhaviSyadvAdinO bhUpatayazca draSTumicchantOpi draSTuM na prApnuvan, yuSmAbhi ryA yAH kathAzca zrUyantE tAH zrOtumicchantOpi zrOtuM nAlabhanta|
Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
25 anantaram EkO vyavasthApaka utthAya taM parIkSituM papraccha, hE upadEzaka anantAyuSaH prAptayE mayA kiM karaNIyaM? (aiōnios )
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
26 yIzuH pratyuvAca, atrArthE vyavasthAyAM kiM likhitamasti? tvaM kIdRk paThasi?
Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
27 tataH sOvadat, tvaM sarvvAntaHkaraNaiH sarvvaprANaiH sarvvazaktibhiH sarvvacittaizca prabhau paramEzvarE prEma kuru, samIpavAsini svavat prEma kuru ca|
Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
28 tadA sa kathayAmAsa, tvaM yathArthaM pratyavOcaH, ittham Acara tEnaiva jIviSyasi|
Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
29 kintu sa janaH svaM nirddOSaM jnjApayituM yIzuM papraccha, mama samIpavAsI kaH? tatO yIzuH pratyuvAca,
Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
30 EkO janO yirUzAlampurAd yirIhOpuraM yAti, Etarhi dasyUnAM karESu patitE tE tasya vastrAdikaM hRtavantaH tamAhatya mRtaprAyaM kRtvA tyaktvA yayuH|
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
31 akasmAd EkO yAjakastEna mArgENa gacchan taM dRSTvA mArgAnyapArzvEna jagAma|
Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
32 ittham EkO lEvIyastatsthAnaM prApya tasyAntikaM gatvA taM vilOkyAnyEna pArzvEna jagAma|
Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
33 kintvEkaH zOmirONIyO gacchan tatsthAnaM prApya taM dRSTvAdayata|
Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
34 tasyAntikaM gatvA tasya kSatESu tailaM drAkSArasanjca prakSipya kSatAni baddhvA nijavAhanOpari tamupavEzya pravAsIyagRham AnIya taM siSEvE|
Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
35 parasmin divasE nijagamanakAlE dvau mudrApAdau tadgRhasvAminE dattvAvadat janamEnaM sEvasva tatra yO'dhikO vyayO bhaviSyati tamahaM punarAgamanakAlE parizOtsyAmi|
Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
36 ESAM trayANAM madhyE tasya dasyuhastapatitasya janasya samIpavAsI kaH? tvayA kiM budhyatE?
“A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
37 tataH sa vyavasthApakaH kathayAmAsa yastasmin dayAM cakAra| tadA yIzuH kathayAmAsa tvamapi gatvA tathAcara|
Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
38 tataH paraM tE gacchanta EkaM grAmaM pravivizuH; tadA marthAnAmA strI svagRhE tasyAtithyaM cakAra|
Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 tasmAt mariyam nAmadhEyA tasyA bhaginI yIzOH padasamIpa uvavizya tasyOpadEzakathAM zrOtumArEbhE|
Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
40 kintu marthA nAnAparicaryyAyAM vyagrA babhUva tasmAddhEtOstasya samIpamAgatya babhASE; hE prabhO mama bhaginI kEvalaM mamOpari sarvvakarmmaNAM bhAram arpitavatI tatra bhavatA kinjcidapi na manO nidhIyatE kim? mama sAhAyyaM karttuM bhavAn tAmAdizatu|
Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
41 tatO yIzuH pratyuvAca hE marthE hE marthE, tvaM nAnAkAryyESu cintitavatI vyagrA cAsi,
Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
42 kintu prayOjanIyam EkamAtram AstE| aparanjca yamuttamaM bhAgaM kOpi harttuM na zaknOti saEva mariyamA vRtaH|
Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”