< yOhanaH 6 >

1 tataH paraM yIzu rgAlIl pradEzIyasya tiviriyAnAmnaH sindhOH pAraM gatavAn|
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 tatO vyAdhimallOkasvAsthyakaraNarUpANi tasyAzcaryyANi karmmANi dRSTvA bahavO janAstatpazcAd agacchan|
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 tatO yIzuH parvvatamAruhya tatra ziSyaiH sAkam|
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 tasmin samaya nistArOtsavanAmni yihUdIyAnAma utsava upasthitE
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 yIzu rnEtrE uttOlya bahulOkAn svasamIpAgatAn vilOkya philipaM pRSTavAn EtESAM bhOjanAya bhOjadravyANi vayaM kutra krEtuM zakrumaH?
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 vAkyamidaM tasya parIkSArtham avAdIt kintu yat kariSyati tat svayam ajAnAt|
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 philipaH pratyavOcat EtESAm EkaikO yadyalpam alpaM prApnOti tarhi mudrApAdadvizatEna krItapUpA api nyUnA bhaviSyanti|
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 zimOn pitarasya bhrAtA AndriyAkhyaH ziSyANAmEkO vyAhRtavAn
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 atra kasyacid bAlakasya samIpE panjca yAvapUpAH kSudramatsyadvayanjca santi kintu lOkAnAM EtAvAtAM madhyE taiH kiM bhaviSyati?
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 pazcAd yIzuravadat lOkAnupavEzayata tatra bahuyavasasattvAt panjcasahastrEbhyO nyUnA adhikA vA puruSA bhUmyAm upAvizan|
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 tatO yIzustAn pUpAnAdAya Izvarasya guNAn kIrttayitvA ziSyESu samArpayat tatastE tEbhya upaviSTalOkEbhyaH pUpAn yathESTamatsyanjca prAduH|
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 tESu tRptESu sa tAnavOcad EtESAM kinjcidapi yathA nApacIyatE tathA sarvvANyavaziSTAni saMgRhlIta|
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 tataH sarvvESAM bhOjanAt paraM tE tESAM panjcAnAM yAvapUpAnAM avaziSTAnyakhilAni saMgRhya dvAdazaPallakAn apUrayan|
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 aparaM yIzOrEtAdRzIm AzcaryyakriyAM dRSTvA lOkA mithO vaktumArEbhirE jagati yasyAgamanaM bhaviSyati sa EvAyam avazyaM bhaviSyadvakttA|
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 ataEva lOkA Agatya tamAkramya rAjAnaM kariSyanti yIzustESAm IdRzaM mAnasaM vijnjAya punazca parvvatam EkAkI gatavAn|
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 sAyaMkAla upasthitE ziSyA jaladhitaTaM vrajitvA nAvamAruhya nagaradizi sindhau vAhayitvAgaman|
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 tasmin samayE timira upAtiSThat kintu yISustESAM samIpaM nAgacchat|
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 tadA prabalapavanavahanAt sAgarE mahAtaraggO bhavitum ArEbhE|
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 tatastE vAhayitvA dvitrAn krOzAn gatAH pazcAd yIzuM jaladhErupari padbhyAM vrajantaM naukAntikam AgacchantaM vilOkya trAsayuktA abhavan
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 kintu sa tAnukttavAn ayamahaM mA bhaiSTa|
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 tadA tE taM svairaM nAvi gRhItavantaH tadA tatkSaNAd uddiSTasthAnE naurupAsthAt|
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 yayA nAvA ziSyA agacchan tadanyA kApi naukA tasmin sthAnE nAsIt tatO yIzuH ziSyaiH sAkaM nAgamat kEvalAH ziSyA agaman Etat pArasthA lOkA jnjAtavantaH|
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 kintu tataH paraM prabhu ryatra Izvarasya guNAn anukIrttya lOkAn pUpAn abhOjayat tatsthAnasya samIpasthativiriyAyA aparAstaraNaya Agaman|
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 yIzustatra nAsti ziSyA api tatra nA santi lOkA iti vijnjAya yIzuM gavESayituM taraNibhiH kapharnAhUm puraM gatAH|
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 tatastE saritpatEH pArE taM sAkSAt prApya prAvOcan hE gurO bhavAn atra sthAnE kadAgamat?
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 tadA yIzustAn pratyavAdId yuSmAnahaM yathArthataraM vadAmi AzcaryyakarmmadarzanAddhEtO rna kintu pUpabhOjanAt tEna tRptatvAnjca mAM gavESayatha|
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 kSayaNIyabhakSyArthaM mA zrAmiSTa kintvantAyurbhakSyArthaM zrAmyata, tasmAt tAdRzaM bhakSyaM manujaputrO yuSmAbhyaM dAsyati; tasmin tAta IzvaraH pramANaM prAdAt| (aiōnios g166)
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios g166)
28 tadA tE'pRcchan IzvarAbhimataM karmma karttum asmAbhiH kiM karttavyaM?
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 tatO yIzuravadad IzvarO yaM prairayat tasmin vizvasanam IzvarAbhimataM karmma|
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 tadA tE vyAharan bhavatA kiM lakSaNaM darzitaM yaddRSTvA bhavati vizvasiSyAmaH? tvayA kiM karmma kRtaM?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 asmAkaM pUrvvapuruSA mahAprAntarE mAnnAM bhOkttuM prApuH yathA lipirAstE| svargIyANi tu bhakSyANi pradadau paramEzvaraH|
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 tadA yIzuravadad ahaM yuSmAnatiyathArthaM vadAmi mUsA yuSmAbhyaM svargIyaM bhakSyaM nAdAt kintu mama pitA yuSmAbhyaM svargIyaM paramaM bhakSyaM dadAti|
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 yaH svargAdavaruhya jagatE jIvanaM dadAti sa IzvaradattabhakSyarUpaH|
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 tadA tE prAvOcan hE prabhO bhakSyamidaM nityamasmabhyaM dadAtu|
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 yIzuravadad ahamEva jIvanarUpaM bhakSyaM yO janO mama sannidhim Agacchati sa jAtu kSudhArttO na bhaviSyati, tathA yO janO mAM pratyEti sa jAtu tRSArttO na bhaviSyati|
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 mAM dRSTvApi yUyaM na vizvasitha yuSmAnaham ityavOcaM|
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 pitA mahyaM yAvatO lOkAnadadAt tE sarvva Eva mamAntikam AgamiSyanti yaH kazcicca mama sannidhim AyAsyati taM kEnApi prakArENa na dUrIkariSyAmi|
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 nijAbhimataM sAdhayituM na hi kintu prErayiturabhimataM sAdhayituM svargAd AgatOsmi|
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 sa yAn yAn lOkAn mahyamadadAt tESAmEkamapi na hArayitvA zESadinE sarvvAnaham utthApayAmi idaM matprErayituH piturabhimataM|
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 yaH kazcin mAnavasutaM vilOkya vizvasiti sa zESadinE mayOtthApitaH san anantAyuH prApsyati iti matprErakasyAbhimataM| (aiōnios g166)
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios g166)
41 tadA svargAd yad bhakSyam avArOhat tad bhakSyam ahamEva yihUdIyalOkAstasyaitad vAkyE vivadamAnA vakttumArEbhirE
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 yUSaphaH putrO yIzu ryasya mAtApitarau vayaM jAnIma ESa kiM saEva na? tarhi svargAd avArOham iti vAkyaM kathaM vaktti?
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 tadA yIzustAn pratyavadat parasparaM mA vivadadhvaM
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 matprErakENa pitrA nAkRSTaH kOpi janO mamAntikam AyAtuM na zaknOti kintvAgataM janaM caramE'hni prOtthApayiSyAmi|
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 tE sarvva IzvarENa zikSitA bhaviSyanti bhaviSyadvAdinAM granthESu lipiritthamAstE atO yaH kazcit pituH sakAzAt zrutvA zikSatE sa Eva mama samIpam AgamiSyati|
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 ya IzvarAd ajAyata taM vinA kOpi manuSyO janakaM nAdarzat kEvalaH saEva tAtam adrAkSIt|
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 ahaM yuSmAn yathArthataraM vadAmi yO janO mayi vizvAsaM karOti sOnantAyuH prApnOti| (aiōnios g166)
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios g166)
48 ahamEva tajjIvanabhakSyaM|
Ni ne burodin rai.
49 yuSmAkaM pUrvvapuruSA mahAprAntarE mannAbhakSyaM bhUkttApi mRtAH
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 kintu yadbhakSyaM svargAdAgacchat tad yadi kazcid bhugkttE tarhi sa na mriyatE|
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 yajjIvanabhakSyaM svargAdAgacchat sOhamEva idaM bhakSyaM yO janO bhugkttE sa nityajIvI bhaviSyati| punazca jagatO jIvanArthamahaM yat svakIyapizitaM dAsyAmi tadEva mayA vitaritaM bhakSyam| (aiōn g165)
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn g165)
52 tasmAd yihUdIyAH parasparaM vivadamAnA vakttumArEbhirE ESa bhOjanArthaM svIyaM palalaM katham asmabhyaM dAsyati?
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 tadA yIzustAn AvOcad yuSmAnahaM yathArthataraM vadAmi manuSyaputrasyAmiSE yuSmAbhi rna bhukttE tasya rudhirE ca na pItE jIvanEna sArddhaM yuSmAkaM sambandhO nAsti|
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 yO mamAmiSaM svAdati mama sudhiranjca pivati sOnantAyuH prApnOti tataH zESE'hni tamaham utthApayiSyAmi| (aiōnios g166)
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios g166)
55 yatO madIyamAmiSaM paramaM bhakSyaM tathA madIyaM zONitaM paramaM pEyaM|
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 yO janO madIyaM palalaM svAdati madIyaM rudhiranjca pivati sa mayi vasati tasminnahanjca vasAmi|
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 matprErayitrA jIvatA tAtEna yathAhaM jIvAmi tadvad yaH kazcin mAmatti sOpi mayA jIviSyati|
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 yadbhakSyaM svargAdAgacchat tadidaM yanmAnnAM svAditvA yuSmAkaM pitarO'mriyanta tAdRzam idaM bhakSyaM na bhavati idaM bhakSyaM yO bhakSati sa nityaM jIviSyati| (aiōn g165)
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 yadA kapharnAhUm puryyAM bhajanagEhE upAdizat tadA kathA EtA akathayat|
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 tadEtthaM zrutvA tasya ziSyANAm anEkE parasparam akathayan idaM gAPhaM vAkyaM vAkyamIdRzaM kaH zrOtuM zakruyAt?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 kintu yIzuH ziSyANAm itthaM vivAdaM svacittE vijnjAya kathitavAn idaM vAkyaM kiM yuSmAkaM vighnaM janayati?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 yadi manujasutaM pUrvvavAsasthAnam UrdvvaM gacchantaM pazyatha tarhi kiM bhaviSyati?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 Atmaiva jIvanadAyakaH vapu rniSphalaM yuSmabhyamahaM yAni vacAMsi kathayAmi tAnyAtmA jIvananjca|
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 kintu yuSmAkaM madhyE kEcana avizvAsinaH santi kE kE na vizvasanti kO vA taM parakarESu samarpayiSyati tAn yIzurAprathamAd vEtti|
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 aparamapi kathitavAn asmAt kAraNAd akathayaM pituH sakAzAt zakttimaprApya kOpi mamAntikam AgantuM na zaknOti|
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 tatkAlE'nEkE ziSyA vyAghuTya tEna sArddhaM puna rnAgacchan|
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 tadA yIzu rdvAdazaziSyAn ukttavAn yUyamapi kiM yAsyatha?
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 tataH zimOn pitaraH pratyavOcat hE prabhO kasyAbhyarNaM gamiSyAmaH? (aiōnios g166)
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios g166)
69 anantajIvanadAyinyO yAH kathAstAstavaiva| bhavAn amarEzvarasyAbhiSikttaputra iti vizvasya nizcitaM jAnImaH|
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 tadA yIzuravadat kimahaM yuSmAkaM dvAdazajanAn manOnItAn na kRtavAn? kintu yuSmAkaM madhyEpi kazcidEkO vighnakArI vidyatE|
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 imAM kathaM sa zimOnaH putram ISkarIyOtIyaM yihUdAm uddizya kathitavAn yatO dvAdazAnAM madhyE gaNitaH sa taM parakarESu samarpayiSyati|
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)

< yOhanaH 6 >