< gAlAtinaH 2 >

1 anantaraM caturdazasu vatsarESu gatESvahaM barNabbA saha yirUzAlamanagaraM punaragacchaM, tadAnOM tItamapi svasagginam akaravaM|
Bayan shekara goma sha huɗu sai na sāke haurawa zuwa Urushalima, a wannan lokaci na tafi tare da Barnabas. Na kuma ɗauki Titus muka tafi tare.
2 tatkAlE'ham IzvaradarzanAd yAtrAm akaravaM mayA yaH parizramO'kAri kAriSyatE vA sa yanniSphalO na bhavEt tadarthaM bhinnajAtIyAnAM madhyE mayA ghOSyamANaH susaMvAdastatratyEbhyO lOkEbhyO vizESatO mAnyEbhyO narEbhyO mayA nyavEdyata|
Na tafi ne bisa ga wani wahayi. Da na kai can, sai na bayyana musu bisharar da nake wa’azi a cikin Al’ummai. Na yi haka a keɓance a gaban waɗanda suke shugabanni, don tsoro kada gudun da nake yi, ko kuwa na riga na yi, yă zama a banza.
3 tatO mama sahacarastItO yadyapi yUnAnIya AsIt tathApi tasya tvakchEdO'pyAvazyakO na babhUva|
Amma ko Titus ma da yake tare da ni, ba a ce dole sai ya yi kaciya ba, ko da yake shi mutumin Al’ummai ne.
4 yatazchalEnAgatA asmAn dAsAn karttum icchavaH katipayA bhAktabhrAtaraH khrISTEna yIzunAsmabhyaM dattaM svAtantryam anusandhAtuM cArA iva samAjaM prAvizan|
Wannan zancen kaciya ya taso domin waɗansu’yan’uwan ƙarya sun shiga cikinmu domin su yi leƙe a kan’yancin da muke da shi a cikin Kiristi Yesu, su kuma mai da mu bayi.
5 ataH prakRtE susaMvAdE yuSmAkam adhikArO yat tiSThEt tadarthaM vayaM daNPaikamapi yAvad AjnjAgrahaNEna tESAM vazyA nAbhavAma|
Ba mu kuwa ba su zarafi ba ko kaɗan, don gaskiyar bishara ta ci gaba da kasance tare da ku.
6 parantu yE lOkA mAnyAstE yE kEcid bhavEyustAnahaM na gaNayAmi yata IzvaraH kasyApi mAnavasya pakSapAtaM na karOti, yE ca mAnyAstE mAM kimapi navInaM nAjnjApayan|
Game da waɗanda aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne, ko wane ne su, duk ɗaya ne a wurina; gama Allah ba ya nuna bambanci, ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙara mini kome ba.
7 kintu chinnatvacAM madhyE susaMvAdapracAraNasya bhAraH pitari yathA samarpitastathaivAcchinnatvacAM madhyE susaMvAdapracAraNasya bhArO mayi samarpita iti tai rbubudhE|
A maimakon haka, sun ga cewa an danƙa mini hakkin wa’azin bishara ga Al’ummai, kamar yadda aka danƙa wa Bitrus ga Yahudawa.
8 yatazchinnatvacAM madhyE prEritatvakarmmaNE yasya yA zaktiH pitaramAzritavatI tasyaiva sA zakti rbhinnajAtIyAnAM madhyE tasmai karmmaNE mAmapyAzritavatI|
Gama Allah wanda ya yi aiki a cikin hidimar Bitrus a matsayin manzo ga Yahudawa, haka ma ya yi aiki a cikin hidimata a matsayin manzo ga Al’ummai.
9 atO mahyaM dattam anugrahaM pratijnjAya stambhA iva gaNitA yE yAkUb kaiphA yOhan caitE sahAyatAsUcakaM dakSiNahastagrahaMNa vidhAya mAM barNabbAnjca jagaduH, yuvAM bhinnajAtIyAnAM sannidhiM gacchataM vayaM chinnatvacA sannidhiM gacchAmaH,
Yaƙub, Bitrus da Yohanna waɗanda suke fitattun ginshiƙai, sun karɓe ni da Barnabas da hannu biyu biyu sa’ad da suka gane alherin da aka ba ni. Suka kuma yarda cewa ya kamata mu tafi wajen Al’ummai, su kuwa su tafi wajen Yahudawa.
10 kEvalaM daridrA yuvAbhyAM smaraNIyA iti| atastadEva karttum ahaM yatE sma|
Abin da dai suka roƙa shi ne ya kamata mu riƙa tuna da matalauta, abin nan da nake marmarin yi.
11 aparam AntiyakhiyAnagaraM pitara AgatE'haM tasya dOSitvAt samakSaM tam abhartsayaM|
Sa’ad da Bitrus ya zo Antiyok, na tsawata masa ido da ido don laifinsa a fili yake.
12 yataH sa pUrvvam anyajAtIyaiH sArddham AhAramakarOt tataH paraM yAkUbaH samIpAt katipayajanESvAgatESu sa chinnatvagmanuSyEbhyO bhayEna nivRtya pRthag abhavat|
Kafin waɗansu mutane su zo daga wurin Yaƙub, yakan ci abinci tare da Al’ummai. Amma da suka iso, sai ya fara janyewa, ya kuma ware kansa daga wajen Al’ummai domin yana tsoron waɗanda suke ƙungiyar masu kaciya.
13 tatO'parE sarvvE yihUdinO'pi tEna sArddhaM kapaTAcAram akurvvan barNabbA api tESAM kApaTyEna vipathagAmyabhavat|
Sauran Yahudawa suka haɗa kai da shi a munafuncinsa har Barnabas ma ya bauɗe.
14 tatastE prakRtasusaMvAdarUpE saralapathE na carantIti dRSTvAhaM sarvvESAM sAkSAt pitaram uktavAn tvaM yihUdI san yadi yihUdimataM vihAya bhinnajAtIya ivAcarasi tarhi yihUdimatAcaraNAya bhinnajAtIyAn kutaH pravarttayasi?
Da na ga cewa ba sa yin daidai da gaskiyar bishara, sai na ce wa Bitrus a gabansu duka, “Kai mutumin Yahuda ne, duk da haka kana rayuwa kamar Ba’al’umme ba kamar mutumin Yahuda ba. To, yaya aka yi, kana tilasta Al’ummai su bi al’adun Yahudawa?
15 AvAM janmanA yihUdinau bhavAvO bhinnajAtIyau pApinau na bhavAvaH
“Mu da muke Yahudawa ta wurin haihuwa ba Al’ummai masu zunubi ba,
16 kintu vyavasthApAlanEna manuSyaH sapuNyO na bhavati kEvalaM yIzau khrISTE yO vizvAsastEnaiva sapuNyO bhavatIti buddhvAvAmapi vyavasthApAlanaM vinA kEvalaM khrISTE vizvAsEna puNyaprAptayE khrISTE yIzau vyazvasiva yatO vyavasthApAlanEna kO'pi mAnavaH puNyaM prAptuM na zaknOti|
mun san cewa mutum ba ya samun kuɓuta ta wurin kiyaye Doka, sai dai ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu. Saboda haka, mu ma, muka sa bangaskiyarmu cikin Kiristi Yesu don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya cikin Kiristi ba ta wurin kiyaye Doka ba, domin ba wanda zai kuɓuta ta wurin bin Doka.
17 parantu yIzunA puNyaprAptayE yatamAnAvapyAvAM yadi pApinau bhavAvastarhi kiM vaktavyaM? khrISTaH pApasya paricAraka iti? tanna bhavatu|
“In kuwa ya zama muna so mu sami zaman marasa laifi a gaban Allah ta wurin dogara ga Kiristi, sa’an nan an same mu mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, ko wannan zai nuna Kiristi yana ƙarfafa zunubi ke nan? A’a, ko kusa!
18 mayA yad bhagnaM tad yadi mayA punarnirmmIyatE tarhi mayaivAtmadOSaH prakAzyatE|
In na sāke gina abin da na rushe, na zama mai karyar Doka ke nan.
19 ahaM yad IzvarAya jIvAmi tadarthaM vyavasthayA vyavasthAyai amriyE|
“Gama ta wurin Doka na mutu ga Doka saboda in rayu ga Allah.
20 khrISTEna sArddhaM kruzE hatO'smi tathApi jIvAmi kintvahaM jIvAmIti nahi khrISTa Eva madanta rjIvati| sAmprataM sazarIrENa mayA yajjIvitaM dhAryyatE tat mama dayAkAriNi madarthaM svIyaprANatyAgini cEzvaraputrE vizvasatA mayA dhAryyatE|
An gicciye ni tare da Kiristi. Yanzu ba ni ne nake raye ba, Kiristi ne yake raye a cikina. Rayuwar da nake yi a jiki, ina rayuwa ce ta wurin bangaskiya cikin Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni ya kuma ba da kansa domina.
21 ahamIzvarasyAnugrahaM nAvajAnAmi yasmAd vyavasthayA yadi puNyaM bhavati tarhi khrISTO nirarthakamamriyata|
Ba na ajiyar alherin Allah a gefe, gama da a ce ana samun adalci ta wurin Doka, ai, da Kiristi ya mutu a banza ke nan!”

< gAlAtinaH 2 >