< kalasinaH 1 >
1 IzvarasyEcchayA yIzukhrISTasya prEritaH paulastImathiyO bhrAtA ca kalasInagarasthAn pavitrAn vizvastAn khrISTAzritabhrAtRn prati patraM likhataH|
Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,
2 asmAkaM tAta IzvaraH prabhu ryIzukhrISTazca yuSmAn prati prasAdaM zAntinjca kriyAstAM|
Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi. Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.
3 khrISTE yIzau yuSmAkaM vizvAsasya sarvvAn pavitralOkAn prati prEmnazca vArttAM zrutvA
Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku.
4 vayaM sadA yuSmadarthaM prArthanAM kurvvantaH svargE nihitAyA yuSmAkaM bhAvisampadaH kAraNAt svakIyaprabhO ryIzukhrISTasya tAtam IzvaraM dhanyaM vadAmaH|
Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka.
5 yUyaM tasyA bhAvisampadO vArttAM yayA susaMvAdarUpiNyA satyavANyA jnjApitAH
Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar
6 sA yadvat kRsnaM jagad abhigacchati tadvad yuSmAn apyabhyagamat, yUyanjca yad dinam ArabhyEzvarasyAnugrahasya vArttAM zrutvA satyarUpENa jnjAtavantastadArabhya yuSmAkaM madhyE'pi phalati varddhatE ca|
da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta.
7 asmAkaM priyaH sahadAsO yuSmAkaM kRtE ca khrISTasya vizvastaparicArakO ya ipaphrAstad vAkyaM
Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu,
8 yuSmAn AdiSTavAn sa EvAsmAn AtmanA janitaM yuSmAkaM prEma jnjApitavAn|
wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.
9 vayaM yad dinam Arabhya tAM vArttAM zrutavantastadArabhya nirantaraM yuSmAkaM kRtE prArthanAM kurmmaH phalatO yUyaM yat pUrNAbhyAm AtmikajnjAnavuddhibhyAm IzvarasyAbhitamaM sampUrNarUpENAvagacchEta,
Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka.
10 prabhO ryOgyaM sarvvathA santOSajanakanjcAcAraM kuryyAtArthata IzvarajnjAnE varddhamAnAH sarvvasatkarmmarUpaM phalaM phalEta,
Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah.
11 yathA cEzvarasya mahimayuktayA zaktyA sAnandEna pUrNAM sahiSNutAM titikSAnjcAcarituM zakSyatha tAdRzEna pUrNabalEna yad balavantO bhavEta,
Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki
12 yazca pitA tEjOvAsinAM pavitralOkAnAm adhikArasyAMzitvAyAsmAn yOgyAn kRtavAn taM yad dhanyaM vadEta varam EnaM yAcAmahE|
kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske.
13 yataH sO'smAn timirasya karttRtvAd uddhRtya svakIyasya priyaputrasya rAjyE sthApitavAn|
Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna,
14 tasmAt putrAd vayaM paritrANam arthataH pApamOcanaM prAptavantaH|
wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.
15 sa cAdRzyasyEzvarasya pratimUrtiH kRtsnAyAH sRSTErAdikarttA ca|
Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta.
16 yataH sarvvamEva tEna sasRjE siMhAsanarAjatvaparAkramAdIni svargamarttyasthitAni dRzyAdRzyAni vastUni sarvvANi tEnaiva tasmai ca sasRjirE|
Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne.
17 sa sarvvESAm AdiH sarvvESAM sthitikArakazca|
Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe.
18 sa Eva samitirUpAyAstanO rmUrddhA kinjca sarvvaviSayE sa yad agriyO bhavEt tadarthaM sa Eva mRtAnAM madhyAt prathamata utthitO'grazca|
Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici.
19 yata Izvarasya kRtsnaM pUrNatvaM tamEvAvAsayituM
Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi,
20 kruzE pAtitEna tasya raktEna sandhiM vidhAya tEnaiva svargamarttyasthitAni sarvvANi svEna saha sandhApayitunjcEzvarENAbhilESE|
ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.
21 pUrvvaM dUrasthA duSkriyAratamanaskatvAt tasya ripavazcAsta yE yUyaM tAn yuSmAn api sa idAnIM tasya mAMsalazarIrE maraNEna svEna saha sandhApitavAn|
A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku.
22 yataH sa svasammukhE pavitrAn niSkalagkAn anindanIyAMzca yuSmAn sthApayitum icchati|
Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi.
23 kintvEtadarthaM yuSmAbhi rbaddhamUlaiH susthiraizca bhavitavyam, AkAzamaNPalasyAdhaHsthitAnAM sarvvalOkAnAM madhyE ca ghuSyamANO yaH susaMvAdO yuSmAbhirazrAvi tajjAtAyAM pratyAzAyAM yuSmAbhiracalai rbhavitavyaM|
Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.
24 tasya susaMvAdasyaikaH paricArakO yO'haM paulaH sO'ham idAnIm AnandEna yuSmadarthaM duHkhAni sahE khrISTasya klEzabhOgasya yOMzO'pUrNastamEva tasya tanOH samitEH kRtE svazarIrE pUrayAmi ca|
Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya.
25 yata Izvarasya mantraNayA yuSmadartham IzvarIyavAkyasya pracArasya bhArO mayi samapitastasmAd ahaM tasyAH samitEH paricArakO'bhavaM|
Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai.
26 tat nigUPhaM vAkyaM pUrvvayugESu pUrvvapuruSEbhyaH pracchannam AsIt kintvidAnIM tasya pavitralOkAnAM sannidhau tEna prAkAzyata| (aiōn )
Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn )
27 yatO bhinnajAtIyAnAM madhyE tat nigUPhavAkyaM kIdRggauravanidhisambalitaM tat pavitralOkAn jnjApayitum IzvarO'bhyalaSat| yuSmanmadhyavarttI khrISTa Eva sa nidhi rgairavAzAbhUmizca|
Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.
28 tasmAd vayaM tamEva ghOSayantO yad EkaikaM mAnavaM siddhIbhUtaM khrISTE sthApayEma tadarthamEkaikaM mAnavaM prabOdhayAmaH pUrNajnjAnEna caikaikaM mAnavaM upadizAmaH|
Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi.
29 EtadarthaM tasya yA zaktiH prabalarUpENa mama madhyE prakAzatE tayAhaM yatamAnaH zrAbhyAmi|
Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.