< Mathayo 18 >

1 Isala zezyo zezyo abhanafunzi bhenza wha Yesu na humozye, “Yu nanu waligosi huwo mwene wa humwanya?”
Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Wanene mafi girma a mulkin sama?''
2 U Yesu akwizya umwana udodo, ameha pakasi yawo,
Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu,
3 na yanje, “Lyoli ihumbawozya, nkagamtubu na bhe hansi abhana abhadodo sagamwayiweza hawhinjile huwomwene wa Ngolobhi.
ya ce, ''Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.
4 Nesho wowonti wawhiha hansi umwana udodo, umuntu hansi oyo gosi huwomwene wa humwanya.
Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 Na wowonti wahuposhele umwana udodo whitawa lyane ahumposhela nene.
Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni.
6 Ila wowonti wasababisya uwana kati ya weka abha bhabhahuneteha asaliti, yayibha shinza wha muntu oyo iwe igosi lya syela lipinywe msingo yakwe, na hudwinizye mwidimi li bahari.
Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.
7 Aheli honse husababu yisala izya viswe huje saga hulini budi husala ezyo awhenze, ila ahele whakwe muntu ola isala ezyo zibhawhenze kwa ajili yamwene!
Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo!
8 Nkesho inyobhe yaho au inama lyaho nkalyasabisizya aviswe lidumule na litaje uhuli nawe. Shinza hani whaho awe ahinjile huwomi luli bila nyobhe au shilema, kuliko atagwe mwimoto wiwila uli ni nyobhe zyonti au amanama gonti. (aiōnios g166)
Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka. (aiōnios g166)
9 Nkesho iliso lyaho livisizye, lisenye na ulitaje uhutali nawe. Shinza hani huliwe awe uinjile huwoni ni liso lyeka kuliko ataywe mumoto wiwila ali na maso gonti. (Geenna g1067)
Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu. (Geenna g1067)
10 Enyi aje msanzalau weka wabha dodo ebha. Kwa maana ihumbabhawozya aje humwanya huli antumi abhene insiku zyonti bhawhenya sha Baba wane wali humwanya.
Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama.
11 (Simisizya: Amazu gagaloleha hansi gimsitali gwa 11, “Kwa kuwa umwana wa Adamu ahenzele awhaule shila shasha tejile” Sagagaloleshe mnakala nyinza zihale).
[Dan Mutum ya zo ya ceci abinda ya bata].
12 Msabhanshi? Nkesho umuntu alini ngole mya moja, na yeka yawo yatega, eshi sagabhahuzileshe tisini na tisa mwigamba na abhale afwate yeka yitejile?
Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba?
13 Na nkayaga, lyoli ihumbawozya, asongwa kuliko zila tisini na tisa zyasaga zitejile.
In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba.
14 Shesho shesho, saga lugano lwa Baba wenyu wa humwanya aje weka wa dodo ebha ateketele.
Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.
15 Nkesho uholo waho avisizye, bhalaga, unolesye ishida yeleho awe numene lyali mwene. Nkabhahutejelezye, unzabhe umwezizye uholo waho.
Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan.
16 Ila nkasagabhahutejelezye, mweje, uholo weka au uwabhele hani pamo nawe, humalomu gasimisizi bhabhele au bhatatu kila izu liwezizye asimisizwe.
Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.
17 Na nkasholonya ahubhatejelezye wozi ishibhanza iswala elyo, nkesho asholanya tena ashitejelezye ishibhanza, eshi na abhe hansi umuntu upagani na unsonkolozya kodi.
In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.
18 Lyoli ihumbawozya, shoshonti shila shamwayipinya panse na humwanya shayipinywa. Na shoshonti shamwa yisatula panse na humwanya shayisatulwa.
Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama.
19 Eshi ihumbawozya aje abhantu bhabhele pakashi yenyu nkabhetehana pamwanya yiswala lyo lyonti panse lya bhasaya, elyo u Baba wane wahumwanya ayihuliwomba.
Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi.
20 Nkabhabha bhabhele au bhatatu wawongene peka whitawa lyane, ene endi pakasi yawo.
Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su.''
21 Tena u Petro ayenza nahumozye Yesu, “Gosi, halenga uhole wane avwisye nane insamehe? Hata mala saba?”
Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, ''Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?''
22 U Yesu amozya, “Sigiehuwozya mala saba, ila hata sabini mala saba.
Yesu ya amsa ya ce masa, ''Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.
23 Kwa sababu eyo awomwene wa humwanya ni sawa nu mwene omo wahanzaga asahihi sye ihesabu afume whaboyi bhakwe.
Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa.
24 Lwahanda asahihisye ihesabu, uboyi weka bhaneta whamwene wali ahudayi italanta elfu kumi.
Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma.
25 Afwatanaje sagaali ni dala lyalipe, ugosi wakwe alajizizye akazwe, onse wakwe pamo na bhana bhakwe na hantu honti hali naho, na malipo gafanyishe.
Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.
26 Esho uboyi agwiye, akhoma amafugamo whilongo lela lyakwe ayanga, 'Gosi, ubhe na golele pamo nane, na imbahulipe kila hantu.'
Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, “Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba.”
27 Esho ugosi wola uboyi, afwatanaje asukumwi we hani ninkombo, anesheye na husamehe iliga elyo.
Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.
28 Ila uboyi ola asogoye na humwaje weka kati ya boyi bhakwe, wali ahudayi idinali mia. Akwesa, abida whimilo na humozye, 'Ndipe shila shihudai.
Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.'
29 ILa ola uboyi uwamwawo agwiye nahu nsisitizye hani, ayanjile, 'Ubhe nugolele nane, imbahulipe.'
Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'
30 Ila uboyi ola wawhande akhanile. Hubadala yakwe, abhalile na huntaje mwijela, hadi lwayihunipa shila shahudayi.
Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan.
31 Na lwabhalola aboyi bhamwawo shila shishifumiye. Bhasononeshwe hani. Bhahenzele na humozye, ugosi wawo shila hantu hatokeye.
Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.
32 Ndiyo ola ugosi wa boyi ola akwizizye, na humozye, awe boyi mibhi nasamehile ane iliga lyane lyonti kwa sababu wandabhile hani.
Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, ''Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni.
33 Ashi! Sagawahanziwaga abhe ninkombo wha boyi abhamwenyu, hansi ane shanaloleye enkombo awe?
Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'
34 Ugosi wakwe avitilwe na humeshe whabhala bhabhayemva hadi lwailipa ishipimo shonti shadayiwaga.
Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa.
35 Esho shesho Ubaba wane wa humwanya shaihubhawombela, nkesho kila weka wenyu saga ayihusamehe uholo wakwe afume mmoyo genyu.”
Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba.''

< Mathayo 18 >