< Luka 15 >

1 Basi asonjezya abhesonga bhonti na bhala abhibhi bhali bhahukaribira bhamwovwe.
To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa.
2 Afalisayo na simbi bhauna bhayanga, “Omuntu ono abhakaribizya abhe mbibhi nantele alya nabho.”
Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”
3 Wabhabhola omfano ogu wayanga
Yesu ya fadi wannan misali, ya ce,
4 “Wenu hwilimwe yali nengole mia nkatejire emo yasagazileha zira tisini na tisa mwipoli, abhale ayanze ele yetejile hata eyilore?
“Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba?
5 Wape nkashile walola ahubheha mmapongo gakwe ashimile.
Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
6 Nafiha akhaya yakwe, abhakwizya arafiki bhakwe na jirani bhakwe abhabhore shimaji pandwemo nane, afwanaje enjajile engore yane yehatejire.'
In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.'
7 embabhola shesho hwanyibha ashime amwanya kwajili ya bhibhi omo yaramba ashile abhinza tisini na tisa ambao sebhalamba
Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
8 Nu hulino she wele yali nesilinje kumi nkawatezya esilinje emo, sahwasya okhozyo n ahwose mnyumba na hwanze hubidii hata ayilole?
Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba?
9 Na nkashile ayilole abhakwizya arafiki bhakwa na jirani bhakwe abhabhola shimaji pandwemo nane afwanaje enjajile esilinje ela yehatejire.
In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.'
10 Embabhola shesho hulisongwe hwitagalila elya kuwa abha Ngolobhe kwajiri yola obhibhi omo yaramba.”
Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”
11 Wayanga, “Omntu omo alinabhana bhabhele
Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza,
12 ola ododo wabhola oyise, Baba mpele eshemu eye shoma yegwela. Wabhagabhila evintu vyakwe.
sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
13 Hata pitagalila ensiku senyinji ola ododo wabhonganya vyonti wasogora abhale ensi eya ohutari wanankanya eshoma shakwe ohwo humaisha ege uhuni.
Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a.
14 Nawabha anankenye eshoma shonti enzala egosi ehinjiye mnsi ela omwahale wape wanda ahwanze.
Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
15 Wabhala wakhata nokhaya omo owensi ela, wape atwaliile hugonda gwakwe arere engorobhe.
Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci.
16 Wabha atamari alya amakhondo gazyalyanga egorobhe wala nomo omntu yapanga ahantu.
Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
17 Nawasebhelela humwoyo gwakwe ayanjila bhali bhalenga abhomba mbomba hwa babawane bhabhalya eshalye nasagazye nane epa efwa nenzala!
Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa!
18 Embasogole embabhale hwa baba wane na hubhole, “Baba enkosile juu eye mwanya na hwitagalila lyaho.
Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka.
19 Sehwanziwa akwiziwe mwana waho nantele; mbombo neshe abhombambo bhabho.”
Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'”
20 Wasogola wabhala hwa yise. Nalisa hutali oyise wakwe alolile walolela husajire wabhala sashembela wagwele msingo wayayila tee.
Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa.
21 Ola omwana wabhola, 'oyise enkosile juu yemwanya na hwitalila lyaho sehwanziwa akwiziwa mwana waho nantele.'
Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
22 Lelo oyise abhabholele abhombambombo bhakwe, 'leti nanali omwenda gawguli gwinza, mkwenesye peli nepete mshidole na virato.
Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa.
23 Reti endama ela yenonile msizile nate tilye nashime.
Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki!
24 Afwanaje ono omwana wane ali afwiye wape azyoshele. Ali atejira wape abhoneshe bhanda ashanjilile.
Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
25 Basi ola omwana wakwe ogosi ali hugonda. Nali ahwenza napalamile pakhaga ahovwezye amazu ege ngoma na shawa hwanga.
A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye.
26 Wakwizya obhomba mbombo omo wabhozya amambo ego geyenu?
Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa.
27 Wabhola oholo waho ayenzele no yise waho asinziye endama yenonile apwanje amwajile nantele ali mwomi.'
Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
28 Wavitwa wakhana ahwinjile mhati basi oyise wafumire hwonze walabha.
Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi.
29 Wagalula oyise wakwe wayanga, 'Enya ane ebhombeye amaha galenga ega wala senkosile endajizyo zyaho wakati wawonti, lelo sompiye ane enya na ye mbuzi embombe ashime na rafiki bhane.
Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba,
30 Lelo nawenza ono omwana waho yaliye vintu vyaho pandwemo na malaya asinziye omwahale endama yenonile.
amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
31 Wabhola, 'Mwana wane, awe olipandwemo nane ensiku zyonti vyendi navyo vya huliwe.
Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne.
32 Antele abhombe ashima ne shangwe ehali yelazima afwanaje; ali atejile wape abhoneshe.”
Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'”

< Luka 15 >