< Luka 14 >

1 Yabha nawinjila mhati mnyumba eya mntu omo mmiongoni mwagosi abhe Mafarisayo isiku elyatoye, alye eshalye bharibhahuzijira.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 Enya, hwitagalila lyakwe hwalimntu obhino owe safura.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 O Yesu wagalula wabhabhola abhane sheria na Farisayo, “Eshi, shinzi apome isiku Elyatoye, au seshasho?”
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 Abhahale bhapoma wakhata waponia, waruhusu abharaje omwene.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 Wabhabhora wenu kati yenyu ambaye engombe yakwe au edogomi yakwe etumbushiye mwilende wenu yasaga agavumbula isiku elyatoye?”
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 Wape sebhawezizye galule enongwa ezi.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 Abhabhola ofwano bhala bhahanilwe, nalolile nabhasalula amatengo aga hwitangalila wayanga,
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 “Nkoyanilwe no muntu hu harusi, oganje akhala amatengo aga hwitagalila, ogajebhe aje oyanilwe omntu yaheshimiwa ashile awe.
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 Wenza ola yabhanile awe nomwene, nahubhole osegulishe ono esho shobhahwande abhenesoni awene itengo elya hwisalo.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Ila nkoyanwe bhalaga okhala pitengo elya hwisalo, nkashile ola yamwanile abhole, `Rafiki wane, enzaga hwitagalila.” esho pobhabhe nehema hwitagalila elya bhantu wonti bhakheye pandwemo nawe.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 Afanaje kila wahwikuzya ahwisiwa wape wahwiyisya azuviwa. '
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 Wabhola ola ya mwanile nobhomba eshalye esha pasanya au esha nandwebhela, uganje abhakwizye arafiki bhaho wala aholo bhaho wala amwenyu bhaho wala ajirani bhaho bhabhalineshoma wape bhasahenze bhamwana awe wapata alipe.
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 Eshi nobhomba eshikurukuru bhakwizye apena, alema, na viwete avipofu,
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 nawe obhabhe nafu afwanaje ebhoselinahahulipe afwanaje wayilipwa nawayi owazyoshe owelyoli.”
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 Nawe nawovwa ego omo owabhala bhakheye pashalye pandwemo nawo abholele, “Nafu ola yabhalye ibumunda katika Oumwene owa Ngolobhe!”
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 Wabhola omntu omo abhombile eshikurukuru eshigosi, ahanile abhantu abhinji.
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 Wasontezya obhomba mbombo wakwe esala eyeshalye abhabhole bhala bhabhanilwe, `'Enzaji, afwanaje evintu vyonti vibhehwelwe tayari.'
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 Bhahandile bhonti, afumye audhuru hunia emo. Owahwande abholele, 'Enkarile ogonda, ehwanzaje embale endwenye. Ehulabha onsajile.'
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 Owamwabho wayanga, `'Enkarile eng'ombe, ejozi zisanu embala azilenje ehulabha onsajile.'
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 Owamwabho wayanga, 'Enejile oshe, afwatanesho sebwezizye ahwenze.'
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 Ola osontelezi wabhala wabhola ogosi wakwa enongwa zye mambo ego. Basi ola omwanesho nyumba wavitwa, `'Wabhola osontizi wakwe fuma nanali obhale mwidara igosi na mvichochoto evi boma obhalete epa apena, na lema na vipofu na viwete.”
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 Osontizi wayanga, `Gosi ego golajizizye gamalishe abhombeshe, hata sheshi nemo enafasi.'
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 Ogosi wabhola osontezi, 'Fuma hwonze obhale hubalabala na mpaho obhashurutishe ahwinjile mhati, enyumba yane ebhe ememile.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 Eshi embabhola yaje katika bhala bha bhahanilwe sahweli hata omo yabhayilenje eshikurukuru shane. '
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Amabongano aminji nabhali bhahubhenjeya wape, agalushe wabhabhola,
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 'Nkashele omntu nkayeze hwiline wape sahuvitu oyise wakwe, no nyine wakwe, noshe wakwe, na bhana bhakwe, na holo bhakwe abheshilume na bhesheshe- nantele hata enafsi yakwe yoyo sawezizye abha mwanafunzi wane.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 Omntu yoyonti yasayeji eshikhobhohanyo shakwe nahwenzi hwisalo lyane sawezizye abha mwanafunzi wane.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 Eshi wenu kati amwe, nkashile ohwanza azenje omnara yasakhala nasoti na bhazye egharama aje alinavyo evyamalelezye?
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 Asibhe wamenwa amale baada eyazenje omsingi abhantu wonti bhabhalola bhaganda huseshe,
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 bhayanga, Omntu ono ahandile azenje wabha salinamaha aga malezyenje.'
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 Au huli no mwene wele, nkahwanza abhale alwe no mwene owenje yasakhala nsoti na abhombe ajehane, aje omwahale pandwemo na bhantu elfu kumi agawezya atangane nola yahwenza juu yakwe na bhantu elfu ishilini?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 Na nkashile walola sewezizye asontezya oujumbe ogwahwanza eamani omntu ola salihutari.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 Shila omo wenyu yasaleshile vyonti vyalinavyo sawezizye abhe mwanafunzi wane.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 Omwoni hantu ahinza, lelo omwoni nkashile gunanjishe oponyeye nu ili gukhole?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 Seguhwanziwa mnsi wala jaa abhantu bhaitaga hwonze. Yali namakutu agatejezye, na ayovwe.”
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Luka 14 >