< Yohana 18 >

1 O Yesu nayanga enongwa ezi, asogoye na bhanafunzi bhakwe ahwenyezye entebha ye Kidron, hwa hwali ne bustani, huula omwene na bhanafunzi bhakwe bhahinjila muhati yakwe.
Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa.
2 Esheshi ola oYuda, wahanzaga ahugalushe, wope aimenye eshemu eyo, afuatanaje oYesu abhalaga husehemu ela mara hahinji abhalaga na bhanafunzi bhakwe.
Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa.
3 Wope oYuda, nawapata ikundi lya sikari na maofisa afume hwa gosi adimi bhahenza ne tala, ikurunzi ne silaha.
Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.
4 Wope oYesu, ohu amenye shila hantu hahali habhombeha zaidi yakwe ahwifumizye hwitazi na abhabhozya, “Wenu wamuhumwanza?”
Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, ''Wa kuke nema''
5 Wope wajile, oYesu Mnazareti.” O Yesu abhabhozya, “Ane nene” Wope oYuda wagalushe oYesu ahali ayemeleye na asikari bhala.
Suka amsa masa su ka ce, ''Yesu Banazare'' Yesu yace masu, Ni ne'' Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
6 Eshi eshi embabhozya, “Ane nene” bhawela shingunga bhagwa pansi.
Sa'adda ya ce masu, ''Ni ne'', suka koma da baya, suka fadi a kasa.
7 Wabhabhozya nantele, “Wenu wa muhumwanza? Bhope waga nantele “oYesu Munazareti.”
Ya sake tambayarsu kuma, ''Wa ku ke nema?'' su ka ce, ''Yesu Banazare.''
8 O Yesu wabhobhozya, “Embabhozezye aje ana nene; eshi nkashe munaanza ane, bhaleshi ebha abhnje bhabhalaje.”
Yesu ya amsa, ''Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;''
9 Ega gali esho aje lila izu likamilishe; pala nayangaga; hwa bhala bhohampiye, senatezizye hata weka.”
Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, ''Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba.''
10 O Simoni Petro, waali ni panga, wega nahudumule ikutu lya hundeelo oboyi wa Dimi ogosi. Ni tawa lyakwe oboyi ola ali yo Malko.
Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne.
11 O Yesu abhozya oPetro, “Wezya ipanga lyaho hu ala yakwe. Yenu ensamwelee eshikombe shila shampiye oDaada?”
Yesu ya ce wa Bitrus, ''Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
12 Eshi lila ikundi lya skari na jemedari, na boyi bha Yahudi, bhakhata oYesu na hupinye.
Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi.
13 Wope walongola nasoti pa hwa Anasi, amwane ali khoi wa Kayaafa, ola wali wa Dimi ogosi omwaha ogwo.
Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan.
14 O Kayafa wabhapiye oushauri Ayahudi yahanziwaga aje omuntu omo afwe husababu ya bhantu.
Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
15 O Simoni oPetro alondoleye oYesu, na shesho omwanafunzi wamwabho. Nola omwanafunzi ali afamahamiha hwa dimi ogosi, wope ahinjila pandwemo no Yesu mwibehewa ilya Chungaji ogosi;
Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu;
16 o Petro ali ayemeleye honze hu ndiango. Ola omwanafunzi wa manyishe hwa dimi ogosi, afumile honze abhala ayanje nola oshe oboyi waalindaga ondiango na humwinjizye oPetro.
Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
17 Ola oboyi walindaga ondiango, abhozezye oPetro, “Aje awe solo pandwemo na bhantu bha muntu ono?” Wope ajile, “Ane wenje.”
Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, ''kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?'' Yace ''bani ba.''
18 Na bhala aboyi bha gosi bhahemeleye apantu pala; bhapembile omwoto afuatanaje hwali isasa, na shesho bhali bhahwota omwoto aje apate ilyoto. Wope oPetro ali nabho, ahwote omwoto ali ayemeleye.
To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
19 Odimi ogosi abhozezye oYesu ahusu abhanafunzi bhakwe ne nsambelezyo zyakwe.
babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma.
20 O Yesu ajile, “Enjebho zyezye pazelu ensi; Ane na sambelezezye wilawila mshibhanza na pantu pala Ayahudi pabhabhonganaga. Nane senayanjile lyalyonti.
Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba.
21 Yenu mwabhozezyaga? Bhabhozyaji ahusu hala hanayanjile. Ebha abhantu bhamenye amambo gananjile.
Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
22 O Yesu nahayanga ezyo, omo wa gosi ali ayemeleye wa khoma oYesu hu khono ogwakwe na pamande waga, “Esho, shashi hwanziwa ahugamule odimi ogosi?”
Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, ''Kana amsa wa babban firist haka.''
23 Wope oYesu ajile, “Nkashe enjanjile enongwa zyazyonti embibhi obhe keti hwego amabhibhi, na nkashe egomoye shinza yenu ekhomwa?
Yesu ya amsa masa yace, ''Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?''
24 O Anasi atwala oYesu hwa Kayafa hwa chungaji ogosi ali afungulwe.
Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
25 O Simoni oPetro ali ayemeleye wahwikosya ilyoto yoyo. Bhala abhantu bhabhozya. “Aje, awe nawe soli pandwemo na bhanafunzi bhakwe?” Wakhana waga, “Ane weenje.”
To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, ''Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?'' Sai yayi musu yace, ''A'a, ba na ciki.''
26 Omo omo waboyi bhachungaji ogosi, waali holo wa lume waadulwe ikutu, ajile, “Se wewe elolile hula hu bustani?”
Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, ''Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?
27 O Petro akhana nantele, na Ehanda ahekuga.
Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
28 Bhahamwega oYesu afume hwa Kayafa paka hu Praitorio. Hwali shapwiti na mazansha. Abhene bhebho sebhahinjiye ePraitorio bhasiye ahwiyonvwe ailye epasaka.
Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa.
29 O Pilato abhabhalilia ahayanga. “Ahaga listako bhole lyalihuhusu omuntu ono?”
Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, 'Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan?'
30 Bhayanga na hubhozye, “Nkashe ono muntu agalisebhomba mbibhi, handa setiletile huliwe.”
''Sai suka amsa suka ce, ''idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka''
31 O Pilato abhabhozya, “Mweji amwe mwemwe, mulonje alengane nendijizyo zyenyu bhope.” Ayahudi bhabhozya, “Endajizyo sezitibhozya abude omuntu wawonti.”
bilatus yace masu, ''Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!'' Sai Yahudawa su kace masa, ''Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa.''
32 Bhayanjile ezi aje izu lya Yesu likamilishe izu lya ayanjile ahusu enfwa yakwe.
Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
33 O Pilato ahinjila nantele hu Praitorio akwizya oYesu; ahabhozya, “Aje, awe oli mwene wa Ayahudi?”
Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, ''kai sarkin Yahudawa ne?''
34 O Yesu ajile, “Aje, awe ombozya ni swali eli ohwanza amanye au afuatanaje bhatumile aje ombozye ane?”
Yesu ya amsa, '' wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?''
35 Wope oPilato ajile, “Ane sendi Yahudi, aje seshashesho?” Ikabela lyenyu no chungaji ogosi ebho bhabhaletile huline; awe obhombile yenu?
Bilatus ya amsa “Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?'' Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. ''Me ka yi?''
36 O Yesu ajile; oumwene wane sewamu omu, nkashe oumwene wane ugaali wa munsi omu aboyi bhane handa bhahomaniye waganje anfume hwa Yahudi. Lyoli oumwene wane seufuma epa” Pansi
Yesu ya amsa, ''Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba.''
37 O Pilato abhozya, “Aje awe eshi oli mwene?” O Yesu ajile, “awe shili shoyanga aje ane endi mwene, afuatana neshi napepwe alenganeshi ane enenzele munsi aje embe keti weela elyoli. Wawonti waali neyo elyoli elitejezya izu lyane.
Sai Bilatus yace masa, ''Wato ashe, sarki ne kai?'' Yesu ya amsa, ''Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata.''
38 O Pilato abhozya, “Elyoli yenu?” Wope nayanga ego ahabhala hwa Yahudi na bhabhozye “Selola nkahamo hwa muntu ono.
Bilatus yace masa, ''Menene gaskiya?'' Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, ''Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba.
39 Amwe mulinoutamaduni wamubhomba emwegulile ofungwa omo owakati we Pasaka. Aje muhwanza aje embigulile omwene wa Yahudi.”
Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?''
40 Bhahomile ekelele bhaile, sio ono, tigulile oBaraba.” Wope oBaraba alifyozi.
Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, ''A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas.'' Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.

< Yohana 18 >