< Псалтирь 66 >
1 Начальнику хора. Песнь. Воскликните Богу, вся земля.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Пойте славу имени Его, воздайте славу, хвалу Ему.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Скажите Богу: как страшен Ты в делах Твоих! По множеству силы Твоей, покорятся Тебе враги Твои.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Вся земля да поклонится Тебе и поет Тебе, да поет имени Твоему!
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Придите и воззрите на дела Бога, страшного в делах над сынами человеческими.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Он превратил море в сушу; через реку перешли стопами, там веселились мы о Нем.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Могуществом Своим владычествует Он вечно; очи Его зрят на народы, да не возносятся мятежники.
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Благословите, народы, Бога нашего и провозгласите хвалу Ему.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Он сохранил душе нашей жизнь и ноге нашей не дал поколебаться.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Ты испытал нас, Боже, переплавил нас, как переплавляют серебро.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Ты ввел нас в сеть, положил оковы на чресла наши,
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 посадил человека на главу нашу. Мы вошли в огонь и в воду, и Ты вывел нас на свободу.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Войду в дом Твой со всесожжениями, воздам Тебе обеты мои,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 которые произнесли уста мои и изрек язык мой в скорби моей.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Всесожжения тучные вознесу Тебе с воскурением тука овнов, принесу в жертву волов и козлов.
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Придите, послушайте, все боящиеся Бога, и я возвещу вам, что сотворил Он для души моей.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Я воззвал к Нему устами моими и превознес Его языком моим.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Если бы я видел беззаконие в сердце моем, то не услышал бы меня Господь.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Но Бог услышал, внял гласу моления моего.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Благословен Бог, Который не отверг молитвы моей и не отвратил от меня милости Своей.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!