< Иисус Навин 9 >

1 Услышав сие, все цари Аморрейские, которые за Иорданом, на горе и на равнине и по всему берегу великого моря, и которые близ Ливана, Хеттеи, Аморреи, Гергесеи, Хананеи, Ферезеи, Евеи и Иевусеи,
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 собрались вместе, дабы единодушно сразиться с Иисусом и Израилем.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 Но жители Гаваона, услышав, что Иисус сделал с Иерихоном и Гаем,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 употребили хитрость: пошли, запаслись хлебом на дорогу и положили ветхие мешки на ослов своих и ветхие, изорванные и заплатанные мехи вина;
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 и обувь на ногах их была ветхая с заплатами, и одежда на них ветхая; и весь дорожный хлеб их был сухой и заплесневелый и раскрошенный.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 Они пришли к Иисусу в стан Израильский в Галгал и сказали ему и всем Израильтянам: из весьма дальней земли пришли мы; итак заключите с нами союз.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 Израильтяне же сказали Евеям: может быть, вы живете близ нас? как нам заключить с вами союз?
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 Они сказали Иисусу: мы рабы твои. Иисус же сказал им: кто вы и откуда пришли?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 Они сказали ему: из весьма дальней земли пришли рабы твои во имя Господа Бога твоего; ибо мы слышали славу Его и все, что сделал Он в Египте,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 и все, что Он сделал двум царям Аморрейским, которые были по ту сторону Иордана, Сигону, царю Есевонскому, и Огу, царю Васанскому, который жил в Астарофе и Едреи.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Слыша сие, старейшины наши и все жители нашей земли сказали нам: возьмите в руки ваши хлеба на дорогу и пойдите навстречу им и скажите им: “мы рабы ваши; итак заключите с нами союз”.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 Этот хлеб наш из домов наших мы взяли теплый в тот день, когда пошли к вам, а теперь вот, он сделался сухой и заплесневелый;
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 и эти мехи с вином, которые мы налили новые, вот, изорвались; и эта одежда наша и обувь наша обветшала от весьма дальней дороги.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 Израильтяне взяли их хлеба, а Господа не вопросили.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 И заключил Иисус с ними мир и постановил с ними условие в том, что он сохранит им жизнь; и поклялись им начальники общества.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 А чрез три дня, как заключили они с ними союз, услышали, что они соседи их и живут близ них;
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 ибо сыны Израилевы, отправившись в путь, пришли в города их на третий день; города же их были: Гаваон, Кефира, Беероф и Кириаф-Иарим.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Иисус и сыны Израилевы не побили их, потому что все начальники общества клялись им Господом Богом Израилевым. За это все общество Израилево возроптало на начальников.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Все начальники сказали всему обществу: мы клялись им Господом Богом Израилевым и потому не можем коснуться их;
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 а вот что сделаем с ними: оставим их в живых, чтобы не постиг нас гнев за клятву, которою мы клялись им.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 И сказали им начальники: пусть они живут, но будут рубить дрова и черпать воду для всего общества. И сделало все общество так, как сказали им начальники.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Иисус призвал их и сказал: для чего вы обманули нас, сказав: “мы весьма далеко от вас”, тогда как вы живете близ нас?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 за это прокляты вы! без конца вы будете рабами, будете рубить дрова и черпать воду для меня и для дома Бога моего!
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Они в ответ Иисусу сказали: дошло до сведения рабов твоих, что Господь Бог твой повелел Моисею, рабу Своему, дать вам всю землю и погубить нас и всех жителей сей земли пред лицом вашим; посему мы весьма боялись, чтобы вы не лишили нас жизни, и сделали это дело;
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 теперь вот мы в руке твоей: как лучше и справедливее тебе покажется поступить с нами, так и поступи.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 И поступил с ними так: избавил их от руки сынов Израилевых, и они не умертвили их;
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 и определил в тот день Иисус, чтобы они рубили дрова и черпали воду для всего общества и для жертвенника Господня; посему жители Гаваона сделались дровосеками и водоносами для жертвенника Божия даже до сего дня, на месте, какое ни избрал бы Господь.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Иисус Навин 9 >