< Иов 31 >
1 Завет положил я с глазами моими, чтобы не помышлять мне о девице.
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Какая же участь мне от Бога свыше? И какое наследие от Вседержителя с небес?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Не для нечестивого ли гибель, и не для делающего ли зло напасть?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Не видел ли Он путей моих, и не считал ли всех моих шагов?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Если я ходил в суете, и если нога моя спешила на лукавство, -
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 пусть взвесят меня на весах правды, и Бог узнает мою непорочность.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Если стопы мои уклонялись от пути и сердце мое следовало за глазами моими, и если что-либо нечистое пристало к рукам моим,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 то пусть я сею, а другой ест, и пусть отрасли мои искоренены будут.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Если сердце мое прельщалось женщиною и я строил ковы у дверей моего ближнего, -
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 пусть моя жена мелет на другого, и пусть другие издеваются над нею,
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 потому что это - преступление, это - беззаконие, подлежащее суду;
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 это - огонь, поядающий до истребления, который искоренил бы все добро мое.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Если я пренебрегал правами слуги и служанки моей, когда они имели спор со мною,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 то что стал бы я делать, когда бы Бог восстал? И когда бы Он взглянул на меня, что мог бы я отвечать Ему?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Не Он ли, Который создал меня во чреве, создал и его и равно образовал нас в утробе?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Отказывал ли я нуждающимся в их просьбе и томил ли глаза вдовы?
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Один ли я съедал кусок мой, и не ел ли от него и сирота?
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 Ибо с детства он рос со мною, как с отцом, и от чрева матери моей я руководил вдову.
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Если я видел кого погибавшим без одежды и бедного без покрова, -
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 не благословляли ли меня чресла его, и не был ли он согрет шерстью овец моих?
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Если я поднимал руку мою на сироту, когда видел помощь себе у ворот,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 то пусть плечо мое отпадет от спины, и рука моя пусть отломится от локтя,
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 ибо страшно для меня наказание от Бога: пред величием Его не устоял бы я.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Полагал ли я в золоте опору мою и говорил ли сокровищу: ты - надежда моя?
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Радовался ли я, что богатство мое было велико, и что рука моя приобрела много?
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Смотря на солнце, как оно сияет, и на луну, как она величественно шествует,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 прельстился ли я в тайне сердца моего, и целовали ли уста мои руку мою?
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Это также было бы преступление, подлежащее суду, потому что я отрекся бы тогда от Бога Всевышнего.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Радовался ли я погибели врага моего и торжествовал ли, когда несчастье постигало его?
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Не позволял я устам моим грешить проклятием души его.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Не говорили ли люди шатра моего: о, если бы мы от мяс его не насытились?
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 Странник не ночевал на улице; двери мои я отворял прохожему.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Если бы я скрывал проступки мои, как человек, утаивая в груди моей пороки мои,
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 то я боялся бы большого общества, и презрение одноплеменников страшило бы меня, и я молчал бы и не выходил бы за двери.
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 О, если бы кто выслушал меня! Вот мое желание, чтобы Вседержитель отвечал мне, и чтобы защитник мой составил запись.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Я носил бы ее на плечах моих и возлагал бы ее, как венец;
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 объявил бы ему число шагов моих, сблизился бы с ним, как с князем.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Если вопияла на меня земля моя и жаловались на меня борозды ее;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 если я ел плоды ее без платы и отягощал жизнь земледельцев,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 то пусть вместо пшеницы вырастает волчец и вместо ячменя куколь. Слова Иова кончились.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.