< Salmos 72 >
1 Por Salomão. Deus, dê ao rei sua justiça; sua justiça para com o filho real.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Ele julgará seu povo com retidão, e seus pobres com justiça.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 As montanhas devem trazer prosperidade para o povo. As colinas trazem o fruto da retidão.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Ele julgará os pobres do povo. Ele salvará as crianças dos necessitados, e quebrará o opressor em pedaços.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Eles o temerão enquanto o sol durar; e enquanto a lua, ao longo de todas as gerações.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Ele descerá como chuva sobre a grama cortada, como chuveiros que regam a terra.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Em seus dias, os justos devem florescer, e abundância de paz, até que a lua não seja mais.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Ele terá domínio também de mar a mar, do rio até os confins da terra.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Those que habitam no deserto se curvarão diante dele. Seus inimigos devem lamber a poeira.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Os reis de Tarshish e das ilhas trarão tributo. Os reis de Sheba e Seba devem oferecer presentes.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Yes, todos os reis devem cair diante dele. Todas as nações devem servi-lo.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Pois ele entregará os necessitados quando ele chorar; os pobres, que não têm nenhum ajudante.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Ele terá piedade dos pobres e necessitados. Ele salvará as almas dos necessitados.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Ele resgatará sua alma da opressão e da violência. O sangue deles será precioso à sua vista.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Ele viverá; e o ouro de Sheba será dado a ele. Os homens rezarão por ele continuamente. Eles o abençoarão durante todo o dia.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Abundância de grãos deve estar em toda a terra. Seus frutos se espalham como o Líbano. Deixe-o florescer, florescendo como a grama do campo.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Seu nome perdura para sempre. Seu nome continua enquanto o sol brilha. Os homens serão abençoados por ele. Todas as nações o chamarão de abençoado.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Louvado seja Deus Iavé, o Deus de Israel, que por si só faz obras maravilhosas.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Bendito seja seu nome glorioso para sempre! Que toda a terra seja preenchida com sua glória! Amém e amém.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 This termina as orações de David, o filho de Jesse.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.