< Salmos 22 >
1 Para o Músico Chefe; definido para “A Corça da Manhã”. Um salmo de David. Meu Deus, meu Deus, por que você me abandonou? Por que você está tão longe de me ajudar, e das palavras do meu gemido?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Meu Deus, eu choro durante o dia, mas você não responde; na estação noturna, e não estou em silêncio.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Mas você é santo, vocês que habitam os louvores de Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Nossos pais confiaram em você. Eles confiaram, e você os entregou.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 They chorou a você, e foram entregues. Eles confiaram em você, e não ficaram desapontados.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Mas eu sou uma minhoca, e nenhum homem; uma censura aos homens, e desprezada pelo povo.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Todos aqueles que me vêem zombar de mim. Eles me insultam com seus lábios. Eles abanam a cabeça, dizendo,
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 “Ele confia em Yahweh. Deixe-o entregá-lo. Deixe-o resgatá-lo, pois ele se deleita com ele”.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Mas você me trouxe para fora do útero. Você me fez confiar enquanto estava nos peitos de minha mãe.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Eu fui jogado em cima de você desde o ventre de minha mãe. Você é meu Deus desde que minha mãe me aborreceu.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Don não estar longe de mim, pois os problemas estão próximos. Pois não há ninguém para ajudar.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many os touros me cercaram. Touros fortes de Bashan me cercaram.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They abrir bem sua boca contra mim, leões que rasgam presas e rugem.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Sou derramado como água. Todos os meus ossos estão fora da articulação. Meu coração é como a cera. Está derretido dentro de mim.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Minha força está seca como um caco. Minha língua gruda no céu da minha boca. Vocês me trouxeram ao pó da morte.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Pois os cães me cercaram. Uma empresa de malfeitores me cercou. Eles perfuraram minhas mãos e meus pés.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Eu posso contar todos os meus ossos. Eles olham e me olham fixamente.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Eles dividem minhas peças de vestuário entre eles. Eles jogam à sorte pela minha roupa.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Mas não esteja muito longe, Yahweh. Você é minha ajuda. Apresse-se para me ajudar!
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Deliver minha alma a partir da espada, minha preciosa vida a partir do poder do cão.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Salve-me da boca do leão! Sim, você me resgatou dos chifres dos bois selvagens.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I declarará seu nome a meus irmãos. Entre a assembléia, eu os elogiarei.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Vós que temeis Yahweh, louvai-o! Todos vocês, descendentes de Jacob, glorifiquem-no! Fiquem admirados com ele, todos vocês descendentes de Israel!
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Pois ele não desprezou nem abominou a aflição dos aflitos, nem escondeu seu rosto dele; mas quando chorou para ele, ele ouviu.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Meus elogios a vocês vêm na grande assembléia. Pagarei meus votos diante daqueles que o temem.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Os humildes devem comer e ficar satisfeitos. Eles elogiarão Iavé que o procura. Deixem seus corações viver para sempre.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Todos os confins da terra devem se lembrar e se voltar para Yahweh. Todos os parentes das nações devem adorar diante de vocês.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Pois o reino é de Yahweh. Ele é o governante sobre as nações.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All os ricos da terra devem comer e adorar. Todos aqueles que descem ao pó devem se curvar diante dele, mesmo aquele que não consegue manter sua alma viva.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Posterity deve servi-lo. As gerações futuras serão informadas sobre o Senhor.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Eles virão e declararão sua retidão a um povo que nascerá, pois ele o fez.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.