< Miquéias 5 >
1 Agora você deve se reunir em tropas, filha de tropas. Ele nos cercou. Eles atacarão o juiz de Israel com uma vara na bochecha.
Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
2 Mas você, Belém Ephrathah, ser pequeno entre os clãs de Judá, de vocês sairá um para mim que será o governante em Israel; cujas saídas são de outrora, de tempos antigos.
“Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
3 Portanto, ele os abandonará até o momento em que ela, que está em trabalho de parto, der à luz. Então o resto de seus irmãos voltará para os filhos de Israel.
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
4 Ele permanecerá de pé e pastoreará na força de Iavé, na majestade do nome de Yahweh seu Deus. Eles viverão, pois então ele será grande até os confins da terra.
Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
5 Ele será nossa paz quando a Assíria invadir nossa terra e quando ele marcha através de nossas fortalezas, então vamos levantar contra ele sete pastores, e oito líderes de homens.
Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
6 Eles governarão a terra da Assíria com a espada, e a terra de Nimrod em seus portões. Ele nos entregará da Assíria, quando ele invade nossa terra, e quando ele marchar dentro de nossa fronteira.
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
7 O remanescente de Jacob estará entre muitos povos como o orvalho de Yahweh, como chuveiros sobre a grama, que não esperam pelo homem nem esperar pelos filhos dos homens.
Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
8 O remanescente de Jacob estará entre as nações, entre muitos povos, como um leão entre os animais da floresta, como um leão jovem entre os rebanhos de ovelhas; que, se ele passar, pisa e rasga em pedaços, e não há ninguém para entregar.
Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
9 Deixe sua mão ser erguida acima de seus adversários, e deixar que todos os seus inimigos sejam cortados.
Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
10 “Isso acontecerá naquele dia”, diz Yahweh, “que eu cortarei seus cavalos dentre vocês e destruirá suas carruagens.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
11 Cortarei as cidades de sua terra e derrubará todas as suas fortalezas.
Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
12 Destruirei a feitiçaria de sua mão. Você não terá adivinhadores.
Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
13 I cortará suas imagens gravadas e seus pilares de entre vocês; e você não mais adorará o trabalho de suas mãos.
Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
14 Desarraigarei seus bastões de Asherah de entre vocês; e eu destruirei suas cidades.
Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
15 I vai executar a vingança com raiva e a ira sobre as nações que não ouviram”.
Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”