< Malaquias 3 >

1 “Eis que eu envio meu mensageiro, e ele preparará o caminho diante de mim! O Senhor, a quem procurais, virá de repente ao seu templo. Eis que o mensageiro do convênio, que desejais, está chegando”, diz Javé dos Exércitos.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 “Mas quem pode suportar o dia de sua vinda? E quem ficará de pé quando ele aparecer? Pois ele é como o fogo de um refinador, e como o sabão de lavadores;
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 e ele se sentará como refinador e purificador de prata, e purificará os filhos de Levi, e os refinará como ouro e prata; e eles oferecerão a Javé ofertas em justiça.
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 Então a oferta de Judá e Jerusalém será agradável a Iavé como nos dias de antigamente e como nos anos antigos.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 Chegarei perto de você para julgar. Serei uma testemunha rápida contra os feiticeiros, contra os adúlteros, contra os perjuros, e contra aqueles que oprimem o mercenário em seu salário, a viúva e o órfão de pai, e que privam o estrangeiro de justiça e não me temem”, diz Yahweh dos exércitos.
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 “Pois eu, Yahweh, não mudo; portanto vocês, filhos de Jacob, não são consumidos.
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Desde os dias de seus pais, vocês se afastaram de minhas ordenanças e não as mantiveram. Voltem para mim, e eu voltarei para vocês”, diz Javé dos Exércitos. “Mas você diz: 'Como retornaremos?'.
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 Será que um homem roubará Deus? No entanto, você me rouba! Mas você diz: “Como nós te roubamos? Em dízimos e ofertas.
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 Vocês estão amaldiçoados com a maldição; por vocês me roubam, até mesmo toda esta nação.
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Tragam o dízimo inteiro para o armazém, para que possa haver comida em minha casa, e testem-me agora nisto”, diz Javé dos Exércitos, “se eu não vos abrir as janelas do céu, e vos derramar uma bênção, que não haverá espaço suficiente para isso”.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Eu repreenderei o devorador por seu bem, e ele não destruirá os frutos de sua terra; nem sua videira lançará seus frutos antes de seu tempo no campo”, diz Yahweh dos Exércitos.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 “Todas as nações vos chamarão abençoados, pois sereis uma terra encantadora”, diz Javé dos Exércitos.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 “Suas palavras foram duras contra mim”, diz Yahweh. “No entanto, você diz: 'O que falamos contra você?
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 Você disse: 'É inútil servir a Deus', e 'De que nos serve que tenhamos seguido suas instruções e que tenhamos caminhado de luto diante de Yahweh dos Exércitos?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 Agora chamamos os orgulhosos de felizes; sim, aqueles que praticam a maldade são construídos; sim, eles tentam a Deus, e escapam”.
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Então aqueles que temiam a Javé falaram uns com os outros; e Javé ouviu e escutou, e um livro de memória foi escrito diante dele para aqueles que temiam a Javé e que honraram seu nome.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 Eles serão meus”, diz Javé dos Exércitos, “minha própria posse no dia em que eu fizer”. Eu os pouparei, como um homem poupa seu próprio filho que o serve”.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 Então você voltará e discernirá entre o justo e o ímpio, entre aquele que serve a Deus e aquele que não o serve.
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malaquias 3 >