< Lucas 19 >

1 Ele entrou e estava de passagem por Jericó.
Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
2 Havia um homem chamado Zacchaeus. Ele era um coletor chefe de impostos e era rico.
Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
3 Ele estava tentando ver quem era Jesus, e não podia por causa da multidão, porque era baixo.
Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
4 Ele correu na frente e subiu em um sicômoro para vê-lo, pois ele ia passar por ali.
Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
5 Quando Jesus chegou ao lugar, olhou para cima e o viu, e lhe disse: “Zaqueu, apressa-te e desce, pois hoje devo ficar em tua casa”.
Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
6 Ele se apressou, desceu e o recebeu alegremente.
Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
7 Quando o viram, todos murmuraram, dizendo: “Ele entrou para alojar-se com um homem que é pecador”.
Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
8 Zaqueu levantou-se e disse ao Senhor: “Eis que, Senhor, metade dos meus bens eu dou aos pobres. Se exiji algo injustamente de alguém, restituo quatro vezes mais”.
Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
9 Jesus lhe disse: “Hoje, a salvação chegou a esta casa, porque ele também é um filho de Abraão.
Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
10 Pois o Filho do Homem veio em busca e para salvar o que estava perdido”.
Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
11 Quando ouviram estas coisas, ele continuou e contou uma parábola, porque estava perto de Jerusalém, e supunham que o Reino de Deus seria revelado imediatamente.
Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
12 Ele disse, portanto, “Um certo nobre foi a um país distante para receber para si um reino e retornar”.
Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
13 Ele chamou dez servos seus e lhes deu dez moedas de mina, e lhes disse: “Façam negócios até eu chegar”.
Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
14 Mas seus cidadãos o odiavam e mandaram um enviado atrás dele, dizendo: 'Não queremos que este homem reine sobre nós'.
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
15 “Quando ele voltou, tendo recebido o reino, ordenou que estes servos, a quem havia dado o dinheiro, fossem chamados a ele, para que ele soubesse o que eles haviam ganho com a condução dos negócios.
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
16 O primeiro veio antes dele, dizendo: 'Senhor, sua mina fez mais dez minas'.
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
17 “Ele disse a ele: 'Muito bem, seu bom servo! Porque você foi encontrado fiel com muito pouco, terá autoridade sobre dez cidades”.
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
18 “O segundo veio, dizendo: 'Sua mina, Senhor, fez cinco minas'.
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
19 “Então ele lhe disse: 'E você deve ter mais de cinco cidades'.
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
20 Veio outro, dizendo: 'Senhor, eis aqui sua mina, que eu guardei em um lenço,
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
21 pois eu o temia, porque você é um homem exigente'. Tu pegas o que não deitaste e colhes o que não semeaste”.
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
22 “Ele lhe disse: 'Da tua própria boca eu te julgarei, seu servo malvado! Você sabia que eu sou um homem exigente, pegando aquilo que eu não deitei e colhendo aquilo que eu não semeei”.
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
23 Então por que você não depositou meu dinheiro no banco, e na minha vinda, eu poderia ter ganho juros sobre ele”.
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
24 Ele disse àqueles que ficaram parados: 'Tire a mina dele e dê a ele que tem as dez minas'.
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
25 “Disseram-lhe: 'Senhor, ele tem dez minas'!
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
26 'Pois eu vos digo que a todos os que têm, será dado mais; mas daquele que não tem, até mesmo o que ele tem lhe será tirado'.
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
27 Mas trazei aqui aqueles meus inimigos que não queriam que eu reinasse sobre eles, e matai-os diante de mim”.
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
28 Having disse estas coisas, ele prosseguiu, subindo para Jerusalém.
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
29 Quando chegou perto de Betfagé e Bethany, na montanha que se chama Olivet, ele enviou dois de seus discípulos,
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
30 dizendo: “Vá para a aldeia do outro lado, na qual, ao entrar, encontrará um potro amarrado, no qual nenhum homem jamais se sentou. Desamarre-o e traga-o.
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
31 Se alguém lhe perguntar: “Por que você o desamarra?”, diga a ele: “O Senhor precisa dele”.
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
32 Aqueles que foram enviados foram embora e encontraram coisas exatamente como ele lhes havia dito.
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
33 Como eles estavam desamarrando o potro, seus donos lhes disseram: “Por que você está desamarrando o potro?
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
34 Eles disseram: “O Senhor precisa disso”.
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
35 Então eles o trouxeram a Jesus. Eles jogaram suas capas sobre o potro e sentaram Jesus sobre eles.
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
36 Enquanto ele ia, eles espalhavam seus mantos na estrada.
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
37 Ao se aproximar, na descida do Monte das Oliveiras, toda a multidão dos discípulos começou a se alegrar e a louvar a Deus com voz alta por todas as obras poderosas que tinham visto,
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
38 dizendo: “Bendito seja o Rei que vem em nome do Senhor! Paz no céu, e glória nas alturas”!
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
39 Alguns dos fariseus da multidão lhe disseram: “Mestre, repreenda seus discípulos”!
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
40 Ele lhes respondeu: “Eu lhes digo que se estas fossem silenciosas, as pedras gritariam”.
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
41 Quando ele se aproximou, viu a cidade e chorou sobre ela,
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
42 dizendo: “Se você, até você, tivesse conhecido hoje as coisas que pertencem à sua paz! Mas agora, elas estão escondidas de seus olhos.
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
43 Pois os dias virão sobre você quando seus inimigos vomitarão uma barricada contra você, o cercarão, o cercarão de todos os lados,
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
44 e o atirarão e seus filhos dentro de você para o chão. Eles não deixarão em você uma pedra sobre outra, porque você não sabia a hora de sua visitação”.
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
45 Ele entrou no templo e começou a expulsar aqueles que nele compravam e vendiam,
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
46 dizendo-lhes: “Está escrito: 'Minha casa é uma casa de oração', mas vocês fizeram dela um 'covil de ladrões'”!
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
47 Ele ensinava diariamente no templo, mas os principais sacerdotes, os escribas e os principais homens entre o povo procuravam destruí-lo.
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
48 Eles não conseguiram encontrar o que poderiam fazer, pois todo o povo se agarrou a cada palavra que ele disse.
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.

< Lucas 19 >