< Levítico 21 >

1 Javé disse a Moisés: “Fala aos sacerdotes, filhos de Aarão, e diz-lhes: 'O sacerdote não se contaminará pelos mortos entre seu povo,
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
2 exceto por seus parentes que lhe são próximos: por sua mãe, por seu pai, por seu filho, por sua filha, por seu irmão,
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 e por sua irmã virgem que lhe é próxima, que não teve marido; por ela ele pode se contaminar.
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
4 Ele não se profanará, sendo um chefe entre seu povo, para profanar-se a si mesmo.
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
5 “'Eles não devem raspar a cabeça ou raspar os cantos da barba ou fazer qualquer corte na carne.
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
6 Serão santos ao seu Deus, e não profanarão o nome do seu Deus, pois oferecerão as ofertas de Javé feitas pelo fogo, o pão do seu Deus. Portanto, serão santos.
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
7 “'Eles não devem se casar com uma mulher que seja prostituta ou profana. Um padre não se casará com uma mulher divorciada de seu marido; pois ele é santo para seu Deus.
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
8 Portanto o santificareis, pois ele oferece o pão de vosso Deus. Ele será santo para vós, pois eu, Yahweh, que vos santifica, sou santo.
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 “'A filha de qualquer padre, se ela se profana fazendo-se de prostituta, ela profana o pai. Ela deve ser queimada com fogo.
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
10 “'Aquele que é o sumo sacerdote entre seus irmãos, sobre cuja cabeça se derrama o óleo da unção, e que se consagra a vestir as vestes, não deixará soltar os cabelos de sua cabeça, nem rasgará suas roupas.
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
11 Ele não deve entrar em nenhum cadáver, nem se contaminar por seu pai ou por sua mãe.
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
12 Ele não deve sair do santuário, nem profanar o santuário de seu Deus; pois a coroa do óleo da unção de seu Deus está sobre ele. Eu sou Yahweh.
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
13 “'Ele deve ter uma esposa na sua virgindade.
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
14 Ele não se casará com uma viúva, ou uma divorciada, ou uma mulher que tenha sido profanada, ou uma prostituta. Ele tomará uma virgem de seu próprio povo como esposa.
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
15 Ele não profanará sua descendência entre seu povo, pois eu sou Yahweh, que o santifica”.
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
16 Yahweh falou a Moisés, dizendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 “Diga a Arão: “Nenhum de seus descendentes através de suas gerações que tem um defeito pode se aproximar para oferecer o pão de seu Deus.
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
18 Para qualquer homem que tenha um defeito, ele não se aproximará: um homem cego, ou coxo, ou que tenha um nariz liso, ou qualquer deformidade,
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
19 ou um homem que tenha um pé ferido, ou uma mão ferida,
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
20 ou corcunda, ou um anão, ou um que tenha um defeito no olho, ou uma doença de coceira, ou crostas, ou que tenha testículos danificados.
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
21 Nenhum homem da descendência de Aarão, o sacerdote que tem um defeito, se aproximará para oferecer as ofertas de Yahweh feitas pelo fogo. Como ele tem um defeito, ele não se aproximará para oferecer o pão de seu Deus.
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
22 Ele comerá o pão de seu Deus, tanto do santíssimo, como do santo.
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
23 Ele não se aproximará do véu, nem do altar, porque tem um defeito; para não profanar meus santuários, pois eu sou Yahweh que os santifica”.
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
24 Então Moisés falou com Arão, com seus filhos e com todos os filhos de Israel.
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.

< Levítico 21 >