< Juízes 9 >

1 Abimelech o filho de Jerubbaal foi a Shechem ter com os irmãos de sua mãe, e falou com eles e com toda a família da casa do pai de sua mãe, dizendo:
Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
2 “Por favor, fale aos ouvidos de todos os homens de Shechem: 'É melhor para você que todos os filhos de Jerubbaal, que são setenta pessoas, governem sobre você, ou que um governe sobre você? Lembre-se também que eu sou seu osso e sua carne”.
“Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
3 Os irmãos de sua mãe falaram dele aos ouvidos de todos os homens de Shechem todas estas palavras. Seus corações inclinados a seguir Abimelech; pois eles disseram: “Ele é nosso irmão”.
Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
4 Eles lhe deram setenta moedas de prata da casa de Baal Berith, com a qual Abimelech contratou companheiros vaidosos e imprudentes que o seguiram.
Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
5 Ele foi à casa de seu pai em Ophrah, e matou seus irmãos, os filhos de Jerubbaal, sendo setenta pessoas, de uma cajadada só; mas Jotham, o filho mais novo de Jerubbaal, ficou, pois ele se escondeu.
Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
6 Todos os homens de Siquém se reuniram com toda a casa de Millo, e foram e fizeram Abimelech rei junto ao carvalho do pilar que estava em Siquém.
Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
7 Quando o disseram a Jotham, ele foi e ficou no topo do Monte Gerizim e levantou sua voz, gritou, e disse-lhes: “Escutem-me, homens de Siquém, para que Deus os escute”.
Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
8 As árvores partiram para ungir um rei sobre si mesmas. Disseram à oliveira: “Reine sobre nós”.
Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
9 “Mas a oliveira lhes disse: “Devo parar de produzir meu azeite, com o qual eles honram a Deus e ao homem por mim, e ir acenar para frente e para trás sobre as árvores?
“Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
10 “As árvores disseram à figueira: “Venha e reine sobre nós”.
“Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
11 “Mas a figueira lhes disse: “Devo deixar minha doçura e meus bons frutos e ir acenar para frente e para trás sobre as árvores?
“Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
12 “As árvores disseram à videira: “Venha e reine sobre nós”.
“Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
13 “A videira disse-lhes: “Devo deixar meu novo vinho, que alegra a Deus e ao homem, e ir acenar para frente e para trás sobre as árvores?
“Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
14 “Então todas as árvores disseram ao silvado: “Venha e reine sobre nós”.
“A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
15 “O silvado disse às árvores: 'Se na verdade me unges rei sobre ti, então vem e refugia-te à minha sombra; e se não, deixa sair fogo do silvado, e devora os cedros do Líbano'.
“Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
16 “Agora, portanto, se você tratou verdadeira e justamente, no sentido de fazer rei Abimelech, e se você tratou bem com Jerubbaal e sua casa, e fez a ele de acordo com o merecimento de suas mãos
“To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
17 (pois meu pai lutou por você, arriscou sua vida, e o libertou da mão de Midian;
a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
18 e você se levantou hoje contra a casa de meu pai e matou seus filhos, setenta pessoas, de uma cajadada só, e fez rei Abimelech, filho de sua serva, sobre os homens de Siquém, porque ele é seu irmão);
(amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
19 se você então lidou verdadeira e justamente com Jerubaal e com sua casa hoje, então alegre-se em Abimeleque, e que ele também se alegre em você;
in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
20 mas se não, que o fogo saia de Abimeleque e devore os homens de Siquém e a casa de Millo; e que o fogo saia dos homens de Siquém e da casa de Millo e devore Abimeleque.”
Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
21 Jotham fugiu e fugiu, e foi para Beer e viveu lá, por medo de Abimelech, seu irmão.
Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
22 Abimelech foi príncipe sobre Israel por três anos.
Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
23 Então Deus enviou um espírito maligno entre Abimeleque e os homens de Siquém; e os homens de Siquém trataram traiçoeiramente Abimeleque,
sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
24 para que a violência feita aos setenta filhos de Jerubaal pudesse vir, e para que seu sangue fosse derramado sobre Abimeleque, seu irmão que os matou, e sobre os homens de Siquém que fortaleceram suas mãos para matar seus irmãos.
Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
25 Os homens de Siquém montaram uma emboscada para ele no topo das montanhas, e roubaram todos os que vieram por ali; e Abimelech foi informado sobre isso.
Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
26 Gaal, filho de Ebed, veio com seus irmãos e foi para Shechem; e os homens de Shechem depositaram nele sua confiança.
To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
27 Eles saíram para o campo, colheram seus vinhedos, pisaram as uvas, comemoraram, entraram na casa de seu deus e comeram e beberam, e amaldiçoaram Abimelech.
Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
28 Gaal o filho de Ebed disse: “Quem é Abimelech, e quem é Shechem, que devemos servi-lo? Ele não é o filho de Jerubbaal? Zebul não é o oficial dele? Servir aos homens de Hamor, o pai de Siquém, mas por que devemos servi-lo?
Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
29 Gostaria que este povo estivesse sob minhas mãos! Então eu removeria Abimelech”. Ele disse a Abimelech: “Aumente seu exército e saia!”
Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
30 Quando Zebul, o governante da cidade, ouviu as palavras de Gaal, o filho de Ebed, sua raiva ardeu.
Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
31 Ele enviou mensageiros a Abimelech com astúcia, dizendo: “Eis que Gaal, filho de Ebede, e seus irmãos chegaram a Siquém; e eis que eles incitam a cidade contra ti.
Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
32 Agora, portanto, suba à noite, você e as pessoas que estão com você, e fique à espera no campo.
To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
33 Será que pela manhã, assim que o sol nascer, vocês se levantarão cedo e se apressarão sobre a cidade. Eis que, quando ele e as pessoas que estão com ele saírem contra vocês, façam a eles o que encontrarem ocasião”.
Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
34 Abimelech se levantou, e todas as pessoas que estavam com ele, à noite, e esperaram contra Shechem em quatro empresas.
Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
35 Gaal, o filho de Ebed, saiu, e ficou na entrada do portão da cidade. Abimelech se levantou, e as pessoas que estavam com ele, da emboscada.
To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
36 Quando Gaal viu o povo, disse a Zebul: “Eis que as pessoas estão descendo dos cumes das montanhas”. Zebul disse-lhe: “Você vê as sombras das montanhas como se fossem homens”.
Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
37 Gaal falou novamente e disse: “Eis que as pessoas estão descendo pelo meio da terra, e uma empresa vem pelo caminho do carvalho de Meonenim”.
Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
38 Então Zebul lhe disse: “Agora onde está sua boca, que você disse: 'Quem é Abimelech, que nós devemos servi-lo? Não é este o povo que você desprezou? Por favor, saia agora e lute com elas”.
Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
39 Gaal saiu antes dos homens de Shechem, e lutou com Abimelech.
Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
40 Abimelech o perseguiu, e ele fugiu diante dele, e muitos caíram feridos, até a entrada do portão.
Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
41 Abimelech vivia em Arumah; e Zebul expulsou Gaal e seus irmãos, para que não morassem em Siquém.
Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
42 No dia seguinte, as pessoas saíram para o campo; e disseram a Abimelech.
Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
43 Ele pegou as pessoas e as dividiu em três empresas, e as colocou à espera no campo; e olhou, e eis que as pessoas saíram da cidade. Então, ele se levantou contra eles e os golpeou.
Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
44 Abimelech e as empresas que estavam com ele correram para frente e ficaram na entrada do portão da cidade; e as duas empresas correram sobre todos os que estavam no campo e os atingiram.
Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
45 Abimelech lutou contra a cidade durante todo aquele dia; e ele tomou a cidade e matou as pessoas dentro dela. Ele derrubou a cidade e a semeou com sal.
Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
46 Quando todos os homens da torre de Shechem ouviram falar dela, entraram na fortaleza da casa de Elberith.
Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
47 Abimelech foi informado de que todos os homens da torre de Shechem estavam reunidos.
Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
48 Abimelech subiu ao Monte Zalmon, ele e todas as pessoas que estavam com ele; e Abimelech pegou um machado na mão, cortou um ramo das árvores, levou-o para cima e o colocou sobre seu ombro. Então ele disse às pessoas que estavam com ele: “O que vocês me viram fazer, apressem-se, e façam como eu fiz!
sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
49 Todas as pessoas do mesmo modo, cada uma cortou seu ramo, seguiu Abimelech, e os colocou na base da fortaleza, e incendiou a fortaleza sobre eles, de modo que todo o povo da torre de Shechem também morreu, cerca de mil homens e mulheres.
Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
50 Então Abimelech foi até Thebez e acampou contra Thebez, e a levou.
Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
51 Mas havia uma torre forte dentro da cidade, e todos os homens e mulheres da cidade fugiram para lá, fecharam-se e subiram para o telhado da torre.
A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
52 Abimelech chegou à torre e lutou contra ela, e se aproximou da porta da torre para queimá-la com fogo.
Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
53 Uma certa mulher jogou uma pedra de moinho superior na cabeça de Abimelech e quebrou seu crânio.
sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
54 Então ele chamou apressadamente o jovem, seu portador de armadura, e lhe disse: “Saque sua espada e mate-me, que os homens não digam de mim: 'Uma mulher o matou'”. Seu jovem o empurrou, e ele morreu”.
Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
55 Quando os homens de Israel viram que Abimelech estava morto, cada um deles partiu para seu lugar.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
56 Thus Deus retribuiu a maldade de Abimeleque, o que ele fez com seu pai ao matar seus setenta irmãos;
Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
57 e Deus retribuiu toda a maldade dos homens de Siquém sobre suas cabeças; e a maldição de Jotão, filho de Jerubbaal, veio sobre eles.
Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.

< Juízes 9 >