< Josué 6 >
1 Agora Jericó estava bem fechada por causa das crianças de Israel. Ninguém saiu, e ninguém entrou.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 Yahweh disse a Josué: “Eis que entreguei Jericó em suas mãos, com seu rei e os poderosos homens de valor.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 Todos os seus homens de guerra devem marchar pela cidade, contornando a cidade uma vez. Vocês farão isso seis dias.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 Sete sacerdotes levarão sete trombetas de chifres de carneiros diante da arca. No sétimo dia, marcharão pela cidade sete vezes, e os sacerdotes tocarão as trombetas.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Será que quando fizerem um longo sopro com a buzina do carneiro, e quando ouvirem o som da trombeta, todo o povo gritará com um grande grito; então a muralha da cidade cairá achatada, e o povo subirá, cada homem em frente a ele”.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Josué, filho de Freira, chamou os sacerdotes e disse-lhes: “Levantem a arca da aliança e deixem sete sacerdotes levar sete trombetas de chifres de carneiros diante da arca de Yahweh”.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 Eles disseram ao povo: “Avancem! Marchem pela cidade e deixem os homens armados passar diante da arca de Yahweh”.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 Foi assim que, quando Josué falou ao povo, os sete sacerdotes com as sete trombetas dos cornos de carneiros antes de Javé avançaram e sopraram as trombetas, e a arca do pacto de Javé as seguiu.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 Os homens armados foram antes dos sacerdotes que tocaram as trombetas, e a arca foi atrás deles. As trombetas soaram enquanto eles iam.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 Josué ordenou ao povo, dizendo: “Não gritarás nem deixarás que tua voz seja ouvida, nem nenhuma palavra sairá de tua boca até o dia em que eu te disser para gritares. Então você gritará”.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 Então ele fez com que a arca de Javé percorresse a cidade, circundando-a uma vez. Então eles entraram no acampamento, e permaneceram no acampamento.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 Josué levantou-se de manhã cedo e os sacerdotes pegaram a arca de Iavé.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 Os sete sacerdotes que levavam as sete trombetas de carneiros em frente à arca de Yahweh continuavam a tocar as trombetas. Os homens armados foram para a frente deles. A retaguarda veio depois da arca de Iavé. As trombetas tocaram enquanto iam.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 No segundo dia, eles marcharam uma vez pela cidade e voltaram ao acampamento. Eles fizeram isso seis dias.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 No sétimo dia, eles se levantaram cedo ao amanhecer do dia, e marcharam pela cidade da mesma forma sete vezes. Neste dia, apenas marcharam pela cidade sete vezes.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 Na sétima vez, quando os sacerdotes tocaram as trombetas, Josué disse ao povo: “Grite, pois Javé lhe deu a cidade!
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 A cidade será dedicada, mesmo ela e tudo o que há nela, a Yahweh. Somente Rahab, a prostituta, viverá, ela e todos que estão com ela em casa, porque escondeu os mensageiros que enviamos.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 Mas, quanto a vocês, apenas se afastem do que é devotado à destruição, para que, quando o tiverem devotado, não tomem do que é devotado; assim fariam o acampamento de Israel amaldiçoado e o perturbariam.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 Mas toda a prata, ouro e vasos de bronze e ferro são sagrados para Iavé. Eles entrarão na tesouraria de Iavé”.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Então o povo gritou e os padres sopraram as trombetas. Quando o povo ouviu o som da trombeta, o povo gritou com um grande grito, e o muro caiu por terra, de modo que o povo subiu na cidade, todos os homens em frente a ele, e tomaram a cidade.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 Eles destruíram completamente tudo o que havia na cidade, tanto homem como mulher, tanto jovem como velho, e boi, ovelha e burro, com o fio da espada.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 Josué disse aos dois homens que haviam espiado a terra: “Entrem na casa da prostituta e tragam a mulher e tudo o que ela tem de lá, como vocês juraram a ela”.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 Os jovens que eram espiões entraram e trouxeram Rahab com seu pai, sua mãe, seus irmãos e tudo o que ela tinha. Eles também trouxeram todos os parentes dela, e os colocaram fora do campo de Israel.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Eles queimaram a cidade com fogo, e tudo o que havia nela. Somente eles colocaram a prata, o ouro e os vasos de bronze e de ferro na tesouraria da casa de Yahweh.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Mas Rahab, a prostituta, a casa de seu pai, e tudo o que ela tinha, Josué salvou vivo. Ela vive no meio de Israel até hoje, porque ela escondeu os mensageiros que Josué enviou para espionar Jericó.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 Josué os comandou com um juramento naquela época, dizendo: “Maldito é o homem diante de Javé que se levanta e constrói esta cidade Jericó. Com a perda de seu primogênito, ele lançará suas bases e, com a perda de seu filho mais novo, erguerá seus portões”.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 Então Yahweh estava com Josué; e sua fama estava em toda a terra.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.