< Jeremias 28 >

1 Nesse mesmo ano, no início do reinado de Zedequias rei de Judá, no quarto ano, no quinto mês, Hananias, filho de Azzur, o profeta, que era de Gibeon, falou comigo na casa de Javé, na presença dos sacerdotes e de todo o povo, dizendo:
A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
2 “Javé dos Exércitos, o Deus de Israel, diz: 'quebrei o jugo do rei da Babilônia.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
3 Dentro de dois anos completos, trarei novamente para este lugar todos os vasos da casa de Iavé que Nabucodonosor, rei da Babilônia, tirou deste lugar e levou para a Babilônia.
Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
4 trarei novamente a este lugar Jeconias, filho de Jeoiaquim, rei de Judá, com todos os cativos de Judá, que foram para a Babilônia”, diz Javé; “pois quebrarei o jugo do rei da Babilônia”.
Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
5 Então o profeta Jeremias disse ao profeta Hananias na presença dos sacerdotes, e na presença de todo o povo que estava na casa de Yahweh,
Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
6 até o profeta Jeremias disse: “Amém! Que Yahweh o faça. Que Javé faça suas palavras que você profetizou, para trazer novamente os vasos da casa de Javé, e todos aqueles que são cativos, da Babilônia para este lugar.
Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
7 Não obstante, escutem agora esta palavra que falo aos vossos ouvidos, e aos ouvidos de todo o povo:
Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
8 Os profetas que foram antes de mim e antes de vós de velhos profetizados contra muitos países, e contra grandes reinos, de guerra, de mal e de pestilência.
Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
9 Quanto ao profeta que profetiza a paz, quando a palavra do profeta acontecer, então o profeta será conhecido, que Iavé o enviou verdadeiramente”.
Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
10 Então Hananiah, o profeta, tirou a barra do pescoço do profeta Jeremias, e a quebrou.
Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
11 Hananias falou na presença de todo o povo, dizendo: “Yahweh diz: 'Mesmo assim quebrarei o jugo de Nabucodonosor, rei da Babilônia, do pescoço de todas as nações, dentro de dois anos inteiros'”. Então o profeta Jeremias seguiu seu caminho.
ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
12 Então a palavra de Javé veio a Jeremias, depois que Hananias o profeta havia quebrado a barra do pescoço do profeta Jeremias, dizendo:
Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 “Vá, e diga a Hananias, dizendo: 'Javé diz: 'Você quebrou as barras de madeira, mas você fez em seu lugar barras de ferro'.
“Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
14 Para Javé dos Exércitos, o Deus de Israel diz: “Coloquei um jugo de ferro no pescoço de todas estas nações, para que sirvam a Nabucodonosor, rei da Babilônia; e eles o servirão”. Eu também lhe dei os animais do campo”””.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
15 Então o profeta Jeremias disse a Hananiah o profeta: “Escuta, Hananiah! Yahweh não o enviou, mas você faz este povo confiar numa mentira.
Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
16 Portanto, Javé diz: “Eis que eu te mandarei para longe da superfície da terra”. Este ano você morrerá, porque falou de rebelião contra Javé”.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
17 Então Hananiah, o profeta, morreu no mesmo ano no sétimo mês.
A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

< Jeremias 28 >