< Isaías 6 >

1 No ano em que o rei Uzziah morreu, eu vi o Senhor sentado em um trono, alto e erguido; e seu trem encheu o templo.
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Acima dele estava o serafim. Cada um tinha seis asas. Com duas ele cobriu seu rosto. Com duas cobriu seus pés. Com dois ele voou.
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 Um chamou o outro, e disse, “Santo, santo, santo, é o Yahweh dos Exércitos! A terra inteira está cheia de sua glória”!
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 Os alicerces das soleiras tremeram com a voz daquele que ligou, e a casa ficou cheia de fumaça.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 Então eu disse: “Ai de mim! Pois estou desfeito, porque sou um homem de lábios impuros e vivo entre um povo de lábios impuros, pois meus olhos viram o Rei, Yahweh dos Exércitos”!
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 Então um dos serafins voou até mim, tendo na mão um carvão vivo, que ele havia tirado com a pinça do altar.
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 Ele tocou minha boca com ela, e disse: “Eis que isto tocou seus lábios; e sua iniqüidade foi tirada, e seu pecado perdoado”.
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 Ouvi a voz do Senhor, dizendo: “A quem enviarei e quem irá por nós”? Então eu disse: “Aqui estou eu”. Mande-me”!
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 Ele disse: “Vá, e diga a esta gente”, Você ouve, de fato, mas não entendem. De fato, você vê, mas não percebe”.
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Engordar o coração deste povo. Deixar seus ouvidos pesados e fechar os olhos; para que eles não vejam com os olhos, ouvem com seus ouvidos, compreender com o coração, e voltar atrás, e ser curado”.
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 Então eu disse: “Senhor, quanto tempo?” Ele respondeu, “Até que as cidades sejam resíduos sem habitantes”, casas sem homem, a terra se torna um desperdício total,
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 e Yahweh afastou os homens para longe, e os lugares abandonados são muitos dentro da terra.
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 Se ainda restar um décimo nele, que, por sua vez, também será consumida, como um terebinto, e como um carvalho cujo toco permanece quando são cortados, assim a semente santa é seu toco”.
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”

< Isaías 6 >