< Isaías 53 >

1 Quem acreditou em nossa mensagem? A quem foi revelado o braço de Yahweh?
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2 Pois ele cresceu antes dele como uma planta terna, e como uma raiz fora do solo seco. Ele não tem boa aparência ou majestade. Quando o vemos, não há beleza que devamos desejar-lhe.
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3 Ele foi desprezado e rejeitada pelos homens, um homem de sofrimento e familiarizado com as doenças. Ele era desprezado como alguém de quem os homens escondem seu rosto; e nós não o respeitamos.
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
4 Certamente ele tem suportado nossa doença e carregou nosso sofrimento; no entanto, nós o consideramos atormentado, atingidos por Deus, e aflitos.
Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
5 Mas ele foi trespassado por nossas transgressões. Ele foi esmagado por nossas iniqüidades. A punição que nos trouxe a paz estava sobre ele; e por suas feridas estamos curados.
Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
6 Tudo o que nós gostamos de ovelhas se extraviou. Cada um se voltou para o seu próprio caminho; e Yahweh colocou sobre ele a iniquidade de todos nós.
Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
7 Ele foi oprimido, no entanto, quando ele foi afligido, não abriu a boca. Como um cordeiro que é levado para o abate, e como uma ovelha que antes de seus tosquiadores está em silêncio, por isso ele não abriu a boca.
Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
8 Ele foi levado pela opressão e pelo julgamento. Quanto à sua geração, que considerou que ele foi cortado da terra dos vivos e atingida pela desobediência do meu povo?
Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
9 Eles fizeram sua sepultura com os ímpios, e com um homem rico em sua morte, embora ele não tivesse feito nenhuma violência, nem havia nenhum engano em sua boca.
Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
10 No entanto, Yahweh gostou de machucá-lo. Ele o fez sofrer. Quando você faz de sua alma uma oferenda pelo pecado, ele verá sua descendência. Ele vai prolongar seus dias e o prazer de Yahweh prosperará em sua mão.
Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
11 Após o sofrimento de sua alma, ele verá a luz e ficará satisfeito. Meu servo justo justificará muitos pelo conhecimento de si mesmo; e ele suportará suas iniqüidades.
Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
12 Portanto, eu lhe darei uma parte com o grande. Ele dividirá o saque com os fortes, porque ele derramou sua alma até a morte e foi contada com os transgressores; mas ele carregava os pecados de muitos e intercedeu pelos transgressores.
Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.

< Isaías 53 >