< Isaías 45 >
1 Yahweh diz a seu ungido, a Cyrus, cuja mão direita segurei para subjugar nações diante dele e despojar reis de suas armaduras, para abrir as portas diante dele, e os portões não devem ser fechados:
“Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
2 “Eu irei antes de você e tornar os lugares ásperos mais suaves. Quebrarei as portas de bronze em pedaços e cortar as barras de ferro.
Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
3 Eu lhe darei os tesouros das trevas e riquezas escondidas de lugares secretos, que você pode saber que sou eu, Yahweh, que o chamo pelo seu nome, até mesmo o Deus de Israel.
Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
4 Para o bem de Jacob meu servo, e Israel, meu escolhido, Eu o chamei pelo seu nome. Eu lhe dei um título, embora você não me conheça.
Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
5 Eu sou Yahweh, e não há mais ninguém. Além de mim, não há Deus. Eu os fortalecerei, embora você não me conheça,
Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
6 que eles podem saber do nascer do sol, e do oeste, que não há ninguém além de mim. Eu sou Yahweh, e não há mais ninguém.
saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
7 Eu formo a luz e criar escuridão. Eu faço a paz e criar uma calamidade. Eu sou Yahweh, que faz todas essas coisas.
Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
8 Chuva, céus, vinda de cima, e deixar os céus derramar a justiça. Deixe a terra se abrir, para que ela possa produzir salvação, e deixar que ela faça surgir a retidão com ela. Eu, Yahweh, o criei.
“Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
9 Ai daquele que se esforça com seu Criador... um pote de barro entre os potes de barro da terra! O barro deve perguntar a ele quem o modela: “O que você está fazendo? ou seu trabalho, “Ele não tem mãos...
“Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
10 Ai daquele que diz a um pai: “De que você se tornou o pai de? ou a uma mãe, “O que você deu à luz?””
Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
11 Yahweh, o Santo de Israel e seu Criador diz: “Você me pergunta sobre as coisas que estão por vir, a respeito de meus filhos”, e vocês me comandam a respeito do trabalho de minhas mãos!
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
12 Eu fiz a terra, e criei o homem sobre ela. Eu, até mesmo minhas mãos, estendi os céus. Eu comandei todo o exército deles.
Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
13 Eu o criei em retidão, e eu vou tornar todos os seus caminhos retos. Ele construirá minha cidade, e deixará meus exilados ir em liberdade, não pelo preço nem pela recompensa”, diz Yahweh dos exércitos.
Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
14 Yahweh diz: “O trabalho do Egito”, e a mercadoria da Etiópia, e os Sabeanos, homens de estatura, virão até você, e eles serão seus. Eles irão atrás de você. Eles devem vir acorrentados. Eles se curvarão diante de você. Eles farão súplicas a você: “Certamente Deus está em você; e não há mais ninguém”. Não há outro deus.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
15 Most certamente você é um Deus que se escondeu, Deus de Israel, o Salvador”.
Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
16 Eles ficarão desapontados, sim, confusos, todos eles. Aqueles que são criadores de ídolos entrarão em confusão juntos.
Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
17 Israel será salvo por Yahweh com uma salvação eterna. Você não ficará desapontado nem confundido com as idades eternas.
Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
18 Para Yahweh, que criou os céus, o Deus que formou a terra e a fez, que a estabeleceram e não a criaram um desperdício, que a formou para ser habitada diz: “Eu sou Yahweh. Não há outro.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
19 Eu não tenho falado em segredo, em um lugar da terra das trevas. Eu não disse à descendência de Jacob: “Procure-me em vão”. Eu, Yahweh, falo a justiça. Declaro que as coisas estão certas.
Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
20 “Reúnam-se e venham. Aproximem-se juntos, vocês que escaparam das nações. Aqueles que não têm conhecimento de quem carrega a madeira de sua imagem gravada, e rezar a um deus que não pode salvar.
“Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
21 Declare e apresente-o. Sim, deixe-os se aconselharem juntos. Quem já mostrou isso desde a antiguidade? Quem o declarou como antigo? Não tenho, Yahweh? Não há outro Deus além de mim, um Deus justo e um Salvador. Não há ninguém além de mim.
Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
22 “Olhe para mim, e seja salvo, todos os confins do mundo; pois eu sou Deus, e não há outro.
“Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
23 Jurei por mim mesmo. A palavra saiu de minha boca em retidão e não será revogada, que para mim cada joelho deve se curvar, cada língua fará um juramento.
Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
24 Eles dirão de mim, “Só há retidão e força em Yahweh”. Até mesmo a ele virão homens. Todos aqueles que se enfureceram contra ele ficarão decepcionados.
Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
25 Toda a descendência de Israel será justificada em Yahweh, e se regozijarão!
Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.