< Isaías 11 >
1 Uma filmagem sairá do estoque da Jesse, e um ramo fora de suas raízes dará frutos.
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
2 O Espírito de Yahweh descansará sobre ele: o espírito de sabedoria e compreensão, o espírito de conselho e poder, o espírito do conhecimento e do medo de Yahweh.
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
3 Seu deleite será o medo de Yahweh. Ele não vai julgar pela visão de seus olhos, nem decidir pela audição de seus ouvidos;
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
4 mas ele julgará os pobres com retidão, e decidir com equidade para os humildes da terra. Ele atingirá a terra com a haste de sua boca; e com o sopro de seus lábios ele matará os ímpios.
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
5 A justiça será o cinto ao redor de sua cintura, e a fidelidade do cinto em torno de sua cintura.
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
6 O lobo vai viver com o cordeiro, e o leopardo se deitará com o cabrito, o bezerro, o leão jovem, e o bezerro engordado juntos; e uma criança pequena os conduzirá.
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
7 A vaca e o urso pastarão. Seus jovens se deitarão juntos. O leão vai comer palha como o boi.
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
8 A criança lactante brincará perto do buraco de uma cobra, e a criança desmamada colocará sua mão na cova da víbora.
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
9 Eles não vão ferir nem destruir em toda a minha montanha sagrada; pois a Terra estará cheia do conhecimento de Yahweh, já que as águas cobrem o mar.
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10 Acontecerá nesse dia que as nações buscarão a raiz de Jessé, que se ergue como bandeira dos povos; e seu lugar de descanso será glorioso.
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
11 Acontecerá nesse dia que o Senhor colocará sua mão novamente na segunda vez para recuperar o que resta de seu povo da Assíria, do Egito, de Pathros, de Cush, de Elam, de Shinar, de Hamath, e das ilhas do mar.
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
12 Ele levantará uma bandeira para as nações, reunirá os párias de Israel e reunirá os dispersos de Judá dos quatro cantos da terra.
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
13 A inveja também de Efraim partirá, e aqueles que perseguem Judá serão cortados. Efraim não invejará Judá, e Judá não perseguirá Efraim.
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
14 Eles voarão sobre os ombros dos filisteus do oeste. Juntos eles saquearão as crianças do leste. Eles estenderão seu poder sobre Edom e Moab, e as crianças de Ammon obedecerão a eles.
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
15 Yahweh destruirá totalmente a língua do mar egípcio; e com seu vento abrasador, agitará sua mão sobre o rio, dividindo-o em sete riachos, e fará com que os homens marchem em sandálias.
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
16 Haverá uma rodovia para o remanescente que resta de seu povo da Assíria, como havia para Israel no dia em que ele saiu da terra do Egito.
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.