< Gênesis 9 >
1 Deus abençoou Noé e seus filhos, e lhes disse: “Sejam fecundos, multipliquem-se e reabasteçam a terra”.
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 O medo de vocês e o pavor de vocês estarão sobre cada animal da terra, e sobre cada ave do céu”. Tudo o que se move ao longo da terra, e todos os peixes do mar, são entregues em suas mãos.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Cada coisa que se move que vive será alimento para você. Como eu lhe dei a erva verde, eu lhe dei tudo a você.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Mas a carne com sua vida, ou seja, seu sangue, você não comerá.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Certamente exigirei a prestação de contas pelo sangue de sua vida. Às mãos de cada animal, eu o requererei. Na mão do homem, mesmo na mão do irmão de cada homem, eu exigirei a vida do homem.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Whoever derrama o sangue do homem, seu sangue será derramado pelo homem, pois Deus fez o homem à sua própria imagem.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Seja fecundo e multiplique. Aumenta abundantemente na terra, e multiplica-te nela”.
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Deus falou a Noé e a seus filhos com ele, dizendo:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 “Quanto a mim, eis que estabeleço minha aliança com você, e com seus descendentes depois de você,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 e com todo ser vivo que está com você: as aves, o gado e todo animal da terra com você, de todos os que saem do navio, até mesmo todo animal da terra.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 Eu estabelecerei meu convênio com vocês: Toda a carne não será mais cortada pelas águas do dilúvio. Nunca mais haverá uma inundação para destruir a terra”.
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Deus disse: “Este é o sinal do pacto que faço entre mim e vós e todo ser vivo que está convosco, por gerações perpétuas”:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 Coloco meu arco-íris na nuvem, e será um sinal de um pacto entre mim e a Terra”.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Quando eu trouxer uma nuvem sobre a terra, que o arco-íris será visto na nuvem,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 eu me lembrarei da minha aliança, que é entre mim e você e todo ser vivo de toda a carne, e as águas não se tornarão mais uma inundação para destruir toda a carne.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 O arco-íris será visto na nuvem. Vou olhar para ele, para que eu possa me lembrar da aliança eterna entre Deus e cada ser vivo de toda a carne que está sobre a terra”.
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Deus disse a Noé: “Este é o símbolo do pacto que estabeleci entre mim e toda a carne que está sobre a terra”.
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Os filhos de Noé que saíram do navio eram Shem, Ham e Japheth. Ham é o pai de Canaã.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Estes três eram os filhos de Noé, e destes a terra inteira foi povoada.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Noé começou a ser agricultor e plantou um vinhedo.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Ele bebeu do vinho e ficou bêbado. Ele foi descoberto dentro de sua tenda.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Ham, o pai de Canaan, viu a nudez de seu pai, e contou aos seus dois irmãos lá fora.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 Shem e Japheth pegaram uma roupa e a colocaram sobre os dois ombros, entraram de costas e cobriram a nudez de seu pai. Seus rostos estavam ao contrário e não viram a nudez do pai.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Noé acordou de seu vinho e sabia o que seu filho mais novo havia feito com ele.
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 Disse ele, “Canaã é amaldiçoada. Ele será um servo de servos para seus irmãos”.
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Ele disse, “Bendito seja Yahweh, o Deus de Shem”. Que Canaan seja seu servo.
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Que Deus amplie o Japheth. Deixe-o morar nas tendas de Shem. Que Canaan seja seu servo”.
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Noé viveu trezentos e cinqüenta anos após a enchente.
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 Todos os dias de Noé foram novecentos e cinqüenta anos, e então ele morreu.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.