< Gênesis 40 >
1 Depois destas coisas, o mordomo do rei do Egito e seu padeiro ofenderam seu senhor, o rei do Egito.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 O Faraó ficou furioso com seus dois oficiais, o copeiro chefe e o padeiro chefe.
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 Ele os colocou sob custódia na casa do capitão da guarda, na prisão, o lugar onde José estava amarrado.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 O capitão da guarda os destinou a Joseph, e ele cuidou deles. Eles permaneceram na prisão por muitos dias.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 Ambos sonharam um sonho, cada homem seu sonho, em uma noite, cada homem de acordo com a interpretação de seu sonho, o portador da taça e o padeiro do rei do Egito, que estavam amarrados na prisão.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 José chegou até eles pela manhã, e os viu, e viu que estavam tristes.
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 Ele perguntou aos oficiais do Faraó que estavam com ele sob custódia na casa de seu mestre, dizendo: “Por que você parece tão triste hoje”?
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 Eles lhe disseram: “Sonhamos um sonho, e não há ninguém que possa interpretá-lo”. Joseph disse-lhes: “As interpretações não pertencem a Deus? Por favor, diga-me isso”.
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 O chefe da copa contou seu sonho a José, e disse-lhe: “Em meu sonho, eis que uma videira estava na minha frente,
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 e na videira havia três ramos. Era como se ela brotasse, florescesse e seus cachos produzissem uvas maduras.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 A taça do Faraó estava na minha mão; e eu peguei as uvas e as espremi na taça do Faraó, e dei a taça na mão do Faraó”.
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Joseph disse-lhe: “Esta é sua interpretação: os três ramos são três dias”.
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 Dentro de mais três dias, o Faraó levantará sua cabeça, e o restituirá ao seu escritório. Você dará a taça do Faraó em sua mão, da mesma forma que você fez quando era seu portador da taça.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Mas lembre-se de mim quando estiver bem com você. Por favor, mostre bondade comigo, faça menção de mim ao Faraó e me tire desta casa.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 Pois de fato, fui roubado da terra dos hebreus, e aqui também nada fiz para que eles me colocassem no calabouço”.
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Quando o padeiro chefe viu que a interpretação era boa, ele disse a Joseph: “Eu também estava em meu sonho, e eis que três cestas de pão branco estavam sobre minha cabeça.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 Na cesta mais alta havia todo tipo de comida cozida para o Faraó, e os pássaros os comiam da cesta na minha cabeça”.
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Joseph respondeu: “Esta é sua interpretação”. As três cestas são de três dias.
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 Dentro de mais três dias, o Faraó levantará sua cabeça de cima de você, e o pendurará em uma árvore; e os pássaros comerão sua carne de cima de você”.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 No terceiro dia, que foi o aniversário do Faraó, ele fez um banquete para todos os seus servos, e levantou a cabeça do copeiro chefe e a cabeça do padeiro chefe entre seus servos.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 Ele restaurou o chefe portador da taça e entregou a taça na mão do Faraó;
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 mas ele enforcou o chefe padeiro, como José havia interpretado para eles.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 No entanto, o chefe da taça não se lembrava de Joseph, mas esqueceu-o.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.