< Ezequiel 36 >

1 Você, filho do homem, profetiza para as montanhas de Israel, e diz: “Vocês, montanhas de Israel, ouçam a palavra de Javé.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 O Senhor Javé diz: 'Porque o inimigo disse contra vocês, “Aha!” e, “Os antigos lugares altos são nossos”!
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 portanto profetiza, e diz: 'O Senhor Javé diz: “Porque, mesmo porque te fizeram desolado, e te engoliram de todos os lados, para que possas ser uma possessão para os resíduos das nações, e tu és tomado nos lábios dos faladores, e o relatório maligno do povo;”
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 portanto, vocês montanhas de Israel, ouçam a palavra do Senhor Javé: O Senhor Javé diz para as montanhas e para as colinas, para os cursos de água e para os vales, para os desertos desolados e para as cidades abandonadas, que se tornaram uma presa e um escárnio para os resíduos das nações que estão ao redor;
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 portanto o Senhor Javé diz “Certamente no fogo do meu ciúme falei contra os resíduos das nações, e contra todos os Edom, que escolheram minha terra para si mesmos para uma possessão com a alegria de todo o seu coração, a despeito da alma, para expulsá-la para uma presa.”’
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 Portanto, profetiza a respeito da terra de Israel, e diz às montanhas, às colinas, aos cursos de água e aos vales: 'O Senhor Javé diz: “Eis que eu falei no meu ciúme e na minha ira, porque suportaste a vergonha das nações”.
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 Portanto, o Senhor Javé diz: “Eu jurei: 'Certamente as nações que estão ao vosso redor suportarão sua vergonha'.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 “““Mas vocês, montanhas de Israel, atirarão seus ramos e darão seus frutos ao meu povo Israel; pois eles estão por vir.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 Pois eis que eu sou por vós, e virei a vós, e sereis lavrados e semeados.
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 multiplicarei homens sobre vós, sobre toda a casa de Israel, até mesmo sobre toda ela. As cidades serão habitadas e os lugares de desperdício serão construídos.
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 Multiplicarei o homem e o animal sobre vocês. Eles aumentarão e serão fecundos. Farei com que vocês sejam habitados como eram antes, e farão melhor do que no início. Então vocês saberão que eu sou Yahweh.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 Yes, farei com que os homens caminhem sobre você, até mesmo meu povo Israel. Eles te possuirão, e tu serás sua herança, e nunca mais os despojarás de seus filhos”.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 “'O Senhor Javé diz: “Porque eles dizem: 'Você é um devorador de homens, e tem sido um desolador de sua nação';
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 portanto, você não devorará mais homens, e não desolará mais sua nação”, diz o Senhor Javé.
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 “Não mais vos deixarei ouvir a vergonha das nações”. Você não mais suportará a censura dos povos, e não fará tropeçar mais sua nação”, diz o Senhor Javé'”.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 Além disso, a palavra de Javé veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 “Filho do homem, quando a casa de Israel vivia em sua própria terra, eles a contaminaram por seus caminhos e por suas obras. Seu caminho diante de mim era como a impureza de uma mulher em sua impureza.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 Portanto, derramei minha ira sobre eles pelo sangue que haviam derramado sobre a terra, e porque o haviam contaminado com seus ídolos.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 Eu os espalhei entre as nações, e eles se dispersaram pelos países. Eu os julguei de acordo com seu modo e de acordo com seus atos.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 Quando chegaram às nações para onde foram, profanaram meu santo nome, na medida em que os homens disseram deles: “Este é o povo de Javé, e deixou sua terra”.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 Mas eu tinha respeito por meu santo nome, que a casa de Israel profanou entre as nações para onde eles foram.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 “Portanto, diga à casa de Israel: 'O Senhor Javé diz: “Eu não faço isso por você, casa de Israel, mas por meu santo nome, que você profanou entre as nações para onde você foi.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 santificarei meu grande nome, que foi profanado entre as nações, o qual profanastes entre elas”. Então as nações saberão que eu sou Yahweh”, diz o Senhor Yahweh, “quando eu for provado santo em vós diante dos seus olhos”.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 “““Pois eu os levarei de entre as nações e os congregarei fora de todos os países, e os trarei para sua própria terra.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 ““Eu aspergirei água limpa sobre vocês, e vocês estarão limpos. Limpar-vos-ei de toda sua sujeira e de todos os vossos ídolos”.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 Também lhes darei um novo coração e porei um novo espírito dentro de vocês. Tirarei de sua carne o coração pedregoso e lhe darei um coração de carne.
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 Colocarei meu Espírito dentro de vós, e vos farei andar nos meus estatutos. Vós guardareis minhas ordenanças e as cumprireis.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 Residirás na terra que dei a teus pais. Vós sereis meu povo e eu serei vosso Deus.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 Eu vos salvarei de toda a vossa impureza. Chamarei pelo grão e o multiplicarei, e não lhe infligirei fome.
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 Multiplicarei o fruto da árvore e o aumento do campo, para que não recebais mais a reprovação da fome entre as nações.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 “““Então vocês se lembrarão de seus maus caminhos e de suas ações que não foram boas; e odiar-se-ão a si mesmos à sua própria vista por suas iniqüidades e por suas abominações.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Não faço isto por vocês”, diz o Senhor Yahweh. “Que isto seja do vosso conhecimento”. Sede envergonhados e confundidos por vossos caminhos, casa de Israel”.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 “'O Senhor Javé diz: “No dia em que eu vos purificar de todas as vossas iniquidades, farei com que as cidades sejam habitadas e os lugares de desperdício sejam construídos.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 A terra que estava desolada será lavrada em vez de ser uma desolação à vista de todos os que por ali passavam.
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 Eles dirão: “Esta terra que estava desolada se tornou como o jardim do Éden”. As cidades desertas, desoladas e arruinadas são fortificadas e habitadas”.
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 Então as nações que ficaram ao seu redor saberão que eu, Javé, construí os lugares arruinados e plantei aquilo que estava desolado. Eu, Yahweh, o disse e o farei”.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 “'O Senhor Javé diz: “Por isso, além disso, serei consultado pela casa de Israel, para fazer isso por eles: Vou aumentá-los com homens como um rebanho”.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 Como o rebanho para sacrifício, como o rebanho de Jerusalém em suas festas designadas, assim as cidades desertas ficarão repletas de rebanhos de homens. Então eles saberão que eu sou Yahweh”.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezequiel 36 >