< Ezequiel 22 >
1 Além disso, a palavra de Javé veio até mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Você, filho do homem, você vai julgar? Você julgará a cidade sangrenta? Então faça com que ela conheça todas as suas abominações.
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Você dirá: 'O Senhor Javé diz: “Uma cidade que derrama sangue dentro de si mesma, para que seu tempo chegue, e que faz ídolos contra si mesma para profaná-la!
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Você se tornou culpada em seu sangue que derramou, e está contaminada em seus ídolos que você fez! Você fez com que seus dias se aproximassem, e chegou ao fim de seus anos. Portanto, fiz de vocês uma reprovação às nações e uma zombaria a todos os países.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Aqueles que estão próximos e aqueles que estão longe de você zombarão de você, seu infame, cheio de tumulto.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 “““Eis que os príncipes de Israel, todos de acordo com seu poder, estiveram em vós para derramar sangue.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 Em vocês eles trataram pai e mãe com desprezo. Entre vós, eles oprimiram o estrangeiro. Em vocês, eles injustiçaram o órfão de pai e a viúva.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Vós desprezastes minhas coisas santas, e profanastes meus sábados.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Homens caluniadores têm estado em vós para derramar sangue. Em você, eles comeram nas montanhas. Eles cometeram lascívia entre vocês.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 Em vocês eles descobriram a nudez de seus pais. Em vocês, eles a humilharam, que estava impura em sua impureza.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 Um cometeu abominação com a mulher de seu vizinho e outro contaminou lascivamente sua nora. Outro em você humilhou sua irmã, a filha de seu pai.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 Em você, eles aceitaram subornos para derramar sangue. Vocês se interessaram e aumentaram, e ganham avidamente de seus vizinhos pela opressão, e me esqueceram”, diz o Senhor Yahweh.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 “““Eis que, portanto, golpeei minha mão em seu ganho desonesto que você fez, e no sangue que foi derramado dentro de você.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Seu coração pode suportar, ou suas mãos podem ser fortes, nos dias em que eu vou lidar com você? Eu, Yahweh, já o disse e o farei.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 Espalharei você entre as nações, e o dispersarei através dos países. Limparei sua imundície de vocês.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 Você será profanado em si mesmo, à vista das nações. Então vocês saberão que eu sou Yahweh””.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 A palavra de Javé veio até mim, dizendo:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Filho do homem, a casa de Israel se tornou uma escória para mim. Todos eles são bronze, estanho, ferro e chumbo no meio da fornalha. Eles são a escória de prata.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Portanto, o Senhor Javé diz: “Porque todos vocês se tornaram escória, portanto, eis que eu os congregarei no meio de Jerusalém”.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 Enquanto recolhem prata, bronze, ferro, chumbo e estanho no meio da fornalha, para soprar o fogo sobre ela, para derretê-la, assim eu vos recolherei em minha ira e em minha ira, e vos porei ali e vos derreterei.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Yes, eu te recolherei, e soprarei sobre ti com o fogo da minha ira, e tu serás derretido no meio dela.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 Como a prata é derretida no meio da fornalha, assim sereis derretidos no meio dela; e sabereis que eu, Yahweh, derramei minha ira sobre vós”.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 A palavra de Yahweh veio até mim, dizendo:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 “Filho do homem, diz-lhe: 'Tu és uma terra que não está limpa nem chovendo no dia da indignação'.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Há uma conspiração de seus profetas dentro dela, como um leão que ruge e devora a presa. Eles devoraram almas. Eles levam tesouros e coisas preciosas. Fizeram muitas viúvas dentro dela.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Seus sacerdotes fizeram violência à minha lei e profanaram minhas coisas sagradas. Eles não fizeram distinção entre o santo e o comum, nem fizeram os homens discernir entre o impuro e o limpo, e esconderam seus olhos de meus sábados. Portanto, eu sou profanado entre eles.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Seus príncipes dentro dela são como lobos devorando a presa, para derramar sangue e destruir almas, para que possam obter ganhos desonestos.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Seus profetas têm emplastrado para eles com cal, vendo falsas visões e adivinhando-lhes mentiras, dizendo: 'O Senhor Javé diz', quando Javé não falou.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 O povo da terra tem usado a opressão e exercido o roubo. Sim, eles perturbaram os pobres e necessitados, e oprimiram o estrangeiro injustamente.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 “Procurei entre eles um homem que construiria o muro e ficaria na brecha diante de mim para a terra, que eu não a destruiria; mas não encontrei ninguém.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Therefore “Derramei minha indignação sobre eles. Eu os consumi com o fogo da minha ira. Trouxe seu próprio caminho sobre suas cabeças”, diz o Senhor Yahweh.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”