< Ezequiel 12 >
1 A palavra de Javé também veio até mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
2 “Filho do homem, você mora no meio da casa rebelde, que tem olhos para ver, e não vê, que tem ouvidos para ouvir, e não ouve; pois eles são uma casa rebelde.
ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
3 “Portanto, você, filho do homem, prepare sua bagagem para a mudança, e mova-se de dia à vista deles. Você deve se mover de seu lugar para outro lugar à vista deles. Pode ser que eles considerem, embora sejam uma casa rebelde.
“Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
4 Você deve trazer sua bagagem de dia à vista deles, como bagagem para a mudança. Você mesmo sairá à noite à vista deles, como quando os homens saem para o exílio.
Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
5 Cavem através da parede à vista deles e levem sua bagagem para fora dessa maneira.
Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
6 À vista deles, você a carregará no ombro e a levará para fora no escuro. Cobrirás teu rosto, para que não vejas a terra, pois eu te coloquei para um sinal à casa de Israel”.
Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
7 Eu o fiz como me foi ordenado. Trouxe minha bagagem de dia, como bagagem para me mover, e à noite escavei a parede com minha mão. Trouxe-a para fora no escuro, e a levei no ombro à vista deles.
Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
8 Pela manhã, a palavra de Javé veio até mim, dizendo:
Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 “Filho do homem, a casa de Israel, a casa rebelde, não lhe disse: 'O que você está fazendo?
“Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
10 “Diga-lhes: 'O Senhor Javé diz: “Este fardo diz respeito ao príncipe em Jerusalém, e a toda a casa de Israel entre os quais estão”.
“Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
11 “Diga: 'Eu sou seu signo. Como eu já fiz, assim será feito com eles. Eles irão para o exílio, para o cativeiro.
Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
12 “'O príncipe que está entre eles levará sua bagagem no ombro no escuro, e sairá. Eles cavarão através da parede para levar as coisas para fora dessa maneira. Ele cobrirá seu rosto, porque não verá a terra com seus olhos.
“Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
13 Também espalharei minha rede sobre ele, e ele será levado na minha armadilha. Eu o levarei à Babilônia para a terra dos caldeus; no entanto, ele não o verá, embora morra lá.
Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
14 Espalharei para cada vento todos os que estão ao seu redor para ajudá-lo, e todas as suas bandas. Eu desembainharei a espada atrás deles.
Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
15 “'Eles saberão que eu sou Yahweh quando eu os dispersar entre as nações e os dispersar pelos países.
“Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
16 Mas deixarei alguns homens deles da espada, da fome e da peste, para que declarem todas as suas abominações entre as nações de onde eles vêm. Então eles saberão que eu sou Yahweh”.
Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
17 Além disso, a palavra de Javé veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Filho do homem, come teu pão com tremor e bebe tua água com tremor e com medo”.
“Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
19 Diga ao povo da terra: “O Senhor Javé diz a respeito dos habitantes de Jerusalém e da terra de Israel”: “Eles comerão seu pão com temor e beberão sua água com consternação, para que sua terra fique desolada, e tudo o que nela existe, por causa da violência de todos os que nela habitam”.
Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
20 As cidades habitadas serão assoladas e a terra será uma desolação. Então vocês saberão que eu sou Yahweh””.
Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
21 A palavra de Javé veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
22 “Filho do homem, que provérbio é esse que você tem na terra de Israel, dizendo: 'Os dias são prolongados, e toda visão falha...'
“Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
23 Diga-lhes portanto: 'O Senhor Javé diz: “Farei cessar este provérbio, e eles não o usarão mais como provérbio em Israel;” mas diga-lhes: 'Os dias estão próximos, e o cumprimento de toda visão.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
24 Pois não haverá mais nenhuma visão falsa nem adivinhação lisonjeadora dentro da casa de Israel”.
Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
25 Pois eu sou Yahweh. Eu falarei, e a palavra que eu falar será executada. Não haverá mais adiamento; pois em vossos dias, casa rebelde, falarei a palavra e a cumprirei”, diz o Senhor Javé'”.
Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
26 Novamente a palavra de Javé veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
27 “Filho do homem, eis que eles da casa de Israel dizem: 'A visão que ele vê está para vir por muitos dias, e ele profetiza de tempos que estão longe'.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
28 “Portanto, diz-lhes: 'O Senhor Javé diz: “Nenhuma das minhas palavras será mais adiada, mas a palavra que eu falar será executada”, diz o Senhor Javé”.
“Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”