< Êxodo 9 >

1 Então Javé disse a Moisés: “Vá até o Faraó e lhe diga: 'Isto é o que Javé, o Deus dos hebreus, diz: “Deixe meu povo ir, para que me sirvam.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
2 Pois se você se recusar a deixá-los ir, e segurá-los quietos,
In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
3 eis que a mão de Javé está no seu gado que está no campo, nos cavalos, nos burros, nos camelos, nos rebanhos e nos rebanhos com uma pestilência muito grave.
hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
4 Yahweh fará uma distinção entre o gado de Israel e o gado do Egito; e nada morrerá de tudo o que pertence aos filhos de Israel””.
Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
5 Yahweh indicou um horário fixo, dizendo: “Amanhã Yahweh fará isto na terra”.
Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
6 Javé fez essa coisa no dia seguinte; e todo o gado do Egito morreu, mas do gado dos filhos de Israel, nem um morreu.
Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
7 Faraó enviou, e eis que não havia tanto como um dos animais de gado dos israelitas mortos. Mas o coração do Faraó era teimoso, e ele não deixou o povo ir.
Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
8 Yahweh disse a Moisés e a Arão: “Pegue um punhado de cinzas da fornalha e deixe Moisés borrifar em direção ao céu à vista do Faraó.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
9 Tornar-se-á pequeno pó sobre toda a terra do Egito, e haverá furúnculos e bolhas que se espalharão sobre o homem e sobre os animais, por toda a terra do Egito”.
Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
10 Eles pegaram as cinzas do forno e se colocaram diante do Faraó; e Moisés aspergiu-o em direção ao céu; e ele se transformou em furúnculos e bolhas que irromperam sobre o homem e sobre os animais.
Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
11 Os magos não puderam estar diante de Moisés por causa das fervuras; pois as fervuras estavam sobre os magos e sobre todos os egípcios.
Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
12 Yahweh endureceu o coração do Faraó, e não os ouviu, como Yahweh havia falado a Moisés.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
13 Yahweh disse a Moisés: “Levanta-te cedo pela manhã, levanta-te diante do Faraó e diz-lhe: 'Isto é o que Yahweh, o Deus dos hebreus, diz: “Deixa o meu povo ir, para que me sirvam.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
14 Por esta vez enviarei todas as minhas pragas contra seu coração, contra seus oficiais e contra seu povo; para que saiba que não há ninguém como eu em toda a terra.
ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
15 Por enquanto eu teria estendido minha mão e teria atingido você e seu povo com pestilência, e você teria sido cortado da terra;
Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
16 mas de fato por esta causa eu o fiz valer: para mostrar-lhe meu poder, e para que meu nome seja declarado em toda a terra,
Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
17 because você ainda se exalta contra meu povo, para que não o deixe ir.
Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
18 Eis que amanhã, por esta ocasião, farei chover uma chuva de granizo muito grave, como não tem acontecido no Egito desde o dia em que foi fundado, até agora.
Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
19 Agora, portanto, ordene que todo o seu gado e tudo o que você tem no campo seja levado para um abrigo. O granizo cairá sobre todo homem e animal que for encontrado no campo, e não for trazido para casa, e eles morrerão”'”.
Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
20 Aqueles que temiam a palavra de Javé entre os servos do faraó fizeram seus servos e seu gado fugir para as casas.
Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
21 Aqueles que não respeitaram a palavra de Iavé deixaram seus servos e seu gado no campo.
Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
22 Yahweh disse a Moisés: “Estende tua mão em direção ao céu, para que possa haver granizo em toda a terra do Egito, sobre o homem, sobre os animais e sobre cada erva do campo, em toda a terra do Egito”.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
23 Moisés estendeu sua vara em direção aos céus, e Javé enviou trovões e granizo; e relâmpagos desceram à terra. Yahweh chovia granizo na terra do Egito.
Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
24 Portanto, houve granizo muito forte, e relâmpagos misturados com o granizo, como não havia estado em toda a terra do Egito desde que se tornou uma nação.
ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
25 O granizo atingiu em toda a terra do Egito tudo o que havia no campo, tanto homem quanto animal; e o granizo atingiu cada erva do campo, e quebrou cada árvore do campo.
Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
26 Somente na terra de Gósen, onde estavam os filhos de Israel, não houve granizo.
Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
27 O Faraó enviou e chamou Moisés e Arão, e disse-lhes: “Desta vez pequei”. Javé é justo e eu e meu povo somos perversos.
Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
28 Reze a Javé, pois já houve trovões e granizo o suficiente. Eu te deixarei ir, e não ficarás mais”.
Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
29 Moisés disse-lhe: “Assim que eu tiver saído da cidade, estenderei minhas mãos para Iavé”. Os trovões cessarão, e não haverá mais granizo; para que saibam que a terra é de Iavé.
Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
30 Mas quanto a você e seus servos, sei que ainda não temem a Deus Yahweh”.
Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
31 O linho e a cevada foram atingidos, pois a cevada havia amadurecido e o linho estava florindo.
(Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
32 Mas o trigo e a espelta não foram batidos, pois não tinham crescido.
Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
33 Moisés saiu da cidade vindo do Faraó, e estendeu suas mãos para Iavé; e os trovões e o granizo cessaram, e a chuva não foi derramada sobre a terra.
Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
34 Quando o Faraó viu que a chuva e o granizo e os trovões tinham cessado, ele pecou ainda mais, e endureceu seu coração, ele e seus servos.
Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
35 O coração do Faraó foi endurecido, e ele não deixou ir os filhos de Israel, assim como Yahweh havia falado através de Moisés.
Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.

< Êxodo 9 >