< Êxodo 17 >

1 Toda a congregação dos filhos de Israel viajou do deserto de Pecado, começando segundo o mandamento de Javé, e acampados em Rephidim; mas não havia água para o povo beber.
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 Portanto, o povo discutiu com Moisés e disse: “Dê-nos água para beber”. Moisés disse a eles: “Por que discutem comigo? Por que vocês testam Yahweh”?
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 O povo estava sedento de água; então o povo murmurou contra Moisés, e disse: “Por que nos trouxeste para fora do Egito, para nos matar, nossos filhos e nosso gado com sede”?
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 Moisés gritou a Javé, dizendo: “O que devo fazer com essas pessoas? Eles estão quase prontos para me apedrejar”.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 Yahweh disse a Moisés: “Caminhe diante do povo, leve consigo os anciãos de Israel, pegue a vara na mão com a qual você bateu no Nilo e vá.
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Eis que estarei ali diante de vós na rocha de Horeb. Baterás na rocha, e dela sairá água, para que o povo possa beber”. Moisés o fez diante dos olhos dos anciãos de Israel.
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 Ele chamou o nome do lugar Massah, e Meribah, porque os filhos de Israel brigaram, e porque testaram Yahweh, dizendo: “Yahweh está entre nós, ou não?
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 Então Amalek veio e lutou com Israel em Rephidim.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 Moisés disse a Josué: “Escolha homens para nós, e saia para lutar com Amalek”. Amanhã estarei no topo da colina com a vara de Deus na mão”.
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 Então Josué fez como Moisés lhe havia dito, e lutou com Amalek; e Moisés, Arão e Hur subiram ao topo da colina.
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 Quando Moisés ergueu sua mão, Israel prevaleceu. Quando ele soltou sua mão, Amalek prevaleceu.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 Mas as mãos de Moisés eram pesadas; então eles pegaram uma pedra e a colocaram debaixo dele, e ele se sentou sobre ela. Aarão e Hur levantaram suas mãos, uma de um lado e a outra do outro. Suas mãos estavam firmes até o pôr-do-sol.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 Josué derrotou Amalek e seu povo com o fio da espada.
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 Yahweh disse a Moisés: “Escreva isto para um memorial em um livro e ensaie nos ouvidos de Josué: que eu apagarei completamente a memória de Amalek de debaixo do céu”.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 Moisés construiu um altar, e chamou seu nome de “Yahweh our Banner”.
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 Ele disse: “Yahweh jurou: 'Yahweh terá guerra com Amalek de geração em geração'”.
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”

< Êxodo 17 >