< Deuteronômio 34 >

1 Moisés subiu das planícies de Moab ao Monte Nebo, até o topo do Pisgah, que fica em frente a Jericó. Yahweh mostrou-lhe toda a terra de Gilead para Dan,
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 e todo o Naftali, e a terra de Efraim e Manasseh, e toda a terra de Judá, para o Mar Ocidental,
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 e o sul, e a planície do vale de Jericó, a cidade das palmeiras, para Zoar.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 Yahweh disse-lhe: “Esta é a terra que jurei a Abraão, a Isaac, e a Jacó, dizendo: 'Eu a darei aos seus descendentes'. Eu vos fiz ver com seus olhos, mas não ireis para lá”.
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 Então Moisés, o servo de Javé, morreu lá na terra de Moab, de acordo com a palavra de Javé.
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 Ele o enterrou no vale na terra de Moab, em frente a Beth Peor, mas nenhum homem sabe onde está seu túmulo até hoje.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 Moisés tinha cento e vinte anos de idade quando morreu. Seu olho não estava escuro, nem sua força tinha desaparecido.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 As crianças de Israel choraram por Moisés nas planícies de Moabe trinta dias, até que os dias de choro no luto por Moisés terminaram.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 Josué, o filho de Freira, estava cheio do espírito de sabedoria, pois Moisés havia colocado suas mãos sobre ele. Os filhos de Israel o escutaram e fizeram como Javé ordenou a Moisés.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 Desde então, não surgiu em Israel um profeta como Moisés, a quem Javé conheceu face a face,
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 em todos os sinais e maravilhas que Javé o enviou para fazer na terra do Egito, ao Faraó e a todos os seus servos, e a toda sua terra,
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 e em todas as mãos poderosas, e em todos os atos espantosos, que Moisés fez aos olhos de todo Israel.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.

< Deuteronômio 34 >