< Deuteronômio 31 >
1 Moisés foi e disse estas palavras a todo Israel.
Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
2 Ele lhes disse: “Hoje tenho cento e vinte anos de idade. Não posso mais sair e entrar”. Javé me disse: “Você não deve passar por este Jordão”.
“Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
3 Yahweh, seu próprio Deus, irá antes de você. Ele destruirá estas nações de antes de você, e você as despojará. Josué passará por diante de vocês, como Javé falou.
Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
4 Yahweh fará com eles como fez com Sihon e com Og, os reis dos amorreus, e com a terra deles, quando os destruiu.
Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
5 Yahweh os entregará diante de vocês, e vocês os farão de acordo com todo o mandamento que eu lhes ordenei.
Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
6 Seja forte e corajoso. Não tenha medo ou medo deles, pois Yahweh, seu próprio Deus, é quem vai com você. Ele não vos faltará nem vos abandonará”.
Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, ba zai taɓa barinku ko yă yashe ku ba.”
7 Moisés chamou Josué, e disse-lhe aos olhos de todo Israel: “Sede fortes e corajosos, porque ireis com este povo à terra que Javé jurou a seus pais dar-lhes; e fareis que a herdem”.
Sai Musa ya kira Yoshuwa, ya ce masa a gaban dukan Isra’ila, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama dole ka tafi tare da mutanen nan zuwa cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse cewa za ba wa kakanninku, dole kuma ka raba ta gare su ta zama gādonsu.
8 O próprio Yahweh é quem vai antes de vocês. Ele estará com vocês. Ele não vos falhará nem vos abandonará. Não tenhais medo. Não se desanimem”.
Ubangiji kansa yana tafe a gabanka, zai kuma kasance tare da kai, ba zai taɓa barinka ko yă yashe ka ba. Kada ka ji tsoro; kada kuma ka karai.”
9 Moisés escreveu esta lei e a entregou aos sacerdotes os filhos de Levi, que levavam a arca do pacto de Iavé, e a todos os anciãos de Israel.
Sai Musa ya rubuta wannan doka ya kuma ba da ita ga firistoci,’ya’yan Lawi maza, waɗanda sukan ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji, da kuma dukan dattawan Isra’ila.
10 Moisés ordenou-lhes, dizendo: “Ao final de cada sete anos, na época estabelecida do ano de libertação, na festa dos estandes,
Sa’an nan Musa ya umarce su ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a shekara ta yafe basusuwa, a lokacin Bikin Tabanakul,
11 quando todo Israel tiver vindo a comparecer diante de Javé, vosso Deus, no lugar que ele escolherá, lereis esta lei diante de todo Israel em sua audiência.
sa’ad da dukan Isra’ila suka zo, don su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa, za ku karanta wannan doka a gabansu, a kunnuwansu.
12 Reúna o povo, os homens, as mulheres e os pequenos, e os estrangeiros que estão dentro de seus portões, para que ouçam, aprendam, temam a Javé seu Deus, e observem fazer todas as palavras desta lei,
Ku tattara mutane, maza, mata da kuma yara, da baƙin da suke zama a cikin garuruwanku, saboda su saurara, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su lura, su bi dukan kalmomin wannan doka.
13 e para que seus filhos, que não conheceram, ouçam e aprendam a temer a Javé seu Deus, desde que vocês vivam na terra onde vocês atravessam o Jordão para possuí-la”.
’Ya’yansu, waɗanda ba su san wannan doka ba, dole su ji ta, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku muddin ranku a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
14 Yahweh disse a Moisés: “Eis que seus dias se aproximam que você deve morrer”. Chamai Josué, e apresentai-vos na Tenda da Reunião, para que eu possa comissioná-lo”. Moisés e Josué foram, e se apresentaram na Tenda da Reunião.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu ranar mutuwarka ta yi kusa. Ka kira Yoshuwa, ku shigo Tentin Sujada, inda zan ba shi ragamar aiki.” Saboda haka Musa da Yoshuwa suka zo, suka kuma shiga Tentin Sujada.
15 Yahweh apareceu na Tenda em um pilar de nuvem, e o pilar de nuvem estava sobre a porta da Tenda.
Ubangiji kuwa ya bayyana a Tentin Sujada a cikin ginshiƙin girgije, sai girgijen ya tsaya a ƙofar Tentin Sujada.
16 Yahweh disse a Moisés: “Eis que dormirás com teus pais”. Este povo se levantará e se fará de prostituta depois dos estranhos deuses da terra para onde vão, e me abandonará e quebrará meu pacto que fiz com eles”.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Za ka huta tare da kakanninka, waɗannan mutane kuwa ba da daɗewa ba za su yi karuwanci ga baƙin alloli na ƙasar da za su shiga. Za su yashe ni su kuma karya alkawarin da na yi da su.
17 Então minha ira se acenderá contra eles naquele dia, e eu os abandonarei, e esconderei meu rosto deles, e eles serão devorados, e muitos males e problemas virão sobre eles; de modo que eles dirão naquele dia: “Estes males não vieram sobre nós porque nosso Deus não está entre nós?”
A wannan rana zan yi fushi da su, in kuma yashe su; zan ɓoye fuskata daga gare su, za a kuwa hallaka su. Masifu masu yawa da wahaloli masu yawa za su auka musu, a wannan rana kuwa za su ce, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu’
18 Certamente esconderei meu rosto naquele dia por todo o mal que eles fizeram, na medida em que se voltaram para outros deuses.
Tabbatacce kuwa, zan ɓoye musu fuskata saboda muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.
19 “Agora, portanto, escrevam esta canção para vocês mesmos, e ensinem-na às crianças de Israel. Ponham-na na boca deles, para que esta canção possa ser para mim uma testemunha contra os filhos de Israel.
“To, sai ka rubuta wannan waƙa domin kanka, ka koya wa Isra’ilawa, ka kuma sa su rera ta, don tă zama shaida a kansu.
20 Pois quando eu os tiver trazido para a terra que jurei a seus pais, que mana leite e mel, e eles comeram e se encheram, e engordaram, então eles se voltarão para outros deuses, e os servirão, e me desprezarão, e quebrarão meu pacto.
Sa’ad da na kawo su cikin ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa ga kakanninsu, sa’ad da kuma suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba, za su juya ga waɗansu alloli su bauta musu, su ƙi ni, su kuma karya alkawarina.
21 Acontecerá que, quando muitos males e problemas se apresentarem, esta canção testemunhará diante deles como testemunha; pois não será esquecida da boca de seus descendentes; pois conheço seus caminhos e o que estão fazendo hoje, antes de trazê-los à terra que lhes prometi”.
Sa’ad da kuma masifu masu yawa da wahaloli masu yawa suka auko musu, wannan waƙa za tă zama shaida a kansu, domin zuriyarsu ba za tă manta da ita ba. Na san abin da za su iya yi, kafin ma in kawo su cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa.”
22 Então Moisés escreveu esta canção no mesmo dia, e a ensinou às crianças de Israel.
Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a wannan rana, ya kuma koya wa Isra’ilawa.
23 Ele encomendou Josué, filho de Freira, e disse: “Sede fortes e corajosos, pois trareis os filhos de Israel para a terra que eu lhes jurei”. Eu estarei com vocês”.
Ubangiji ya ba wa Yoshuwa ɗan Nun wannan umarni, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama za ka kawo Isra’ilawa cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa, ni kaina kuwa zan kasance tare da kai.”
24 Quando Moisés terminou de escrever as palavras desta lei em um livro, até que fossem terminadas,
Bayan Musa ya gama rubuta kalmomin dokan nan a littafi daga farko zuwa ƙarshe,
25 Moisés ordenou aos levitas, que carregavam a arca do pacto de Iavé, dizendo:
sai ya ba wa Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji wannan umarni,
26 “Pegue este livro da lei e coloque-o ao lado da arca do pacto de Iavé seu Deus, para que ele possa estar lá para uma testemunha contra você.
“Ku ɗauki wannan Littafin Doka ku sa shi kusa da akwatin alkawarin Ubangiji Allahnku. A can zai kasance a matsayin shaida a kanku.
27 Pois eu conheço sua rebelião e seu pescoço duro. Eis que, enquanto eu ainda estou vivo com você hoje, você tem sido rebelde contra Javé. Quanto mais depois de minha morte?
Gama na sani yadda kuke’yan tawaye da masu taurinkai. In kuna yin tawaye ga Ubangiji tun ina da rai tare da ku, yaya tawayen da za ku yi masa bayan na rasu!
28 Reúna a mim todos os anciãos de suas tribos e seus oficiais, para que eu possa dizer estas palavras aos seus ouvidos, e chamar o céu e a terra para testemunhar contra eles.
Ku tattara dukan dattawan kabilanku, da kuma dukan hafsoshinku a gabana, saboda in faɗa waɗannan kalmomi a kunnuwansu, in kuma kira ga sama da ƙasa su zama shaida a kansu.
29 Pois eu sei que depois de minha morte vós vos corrompereis totalmente e vos afastareis do caminho que vos ordenei; e o mal vos acontecerá nos últimos dias, porque fareis o que é mau aos olhos de Javé, para provocá-lo à ira através do trabalho de vossas mãos”.
Gama na san cewa bayan rasuwata, tabbatacce za ku lalace gaba ɗaya, ku juye daga hanyar da na umarce ku. A kwanaki masu zuwa, masifa za tă auka muku saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, ku tsokane shi har yă yi fushi ta wurin abin da hannuwanku suka yi.”
30 Moisés falou aos ouvidos de toda a assembléia de Israel as palavras desta canção, até que elas terminassem.
Sai Musa ya karanta kalmomin waƙar daga farko zuwa ƙarshe a kunnuwan dukan taron jama’ar Isra’ila.