< Daniel 11 >

1 “Quanto a mim, no primeiro ano de Darius the Mede, levantei-me para confirmá-lo e fortalecê-lo.
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 “Agora vou mostrar-lhes a verdade. Eis que mais três reis se levantarão na Pérsia. O quarto será muito mais rico do que todos eles. Quando ele se fortalecer através de suas riquezas, ele agitará todos contra o reino da Grécia.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 Um rei poderoso se levantará, que reinará com grande domínio, e fará de acordo com sua vontade.
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 Quando ele se levantar, seu reino será quebrado e será dividido para os quatro ventos do céu, mas não para sua posteridade, nem de acordo com seu domínio com o qual ele governou; pois seu reino será arrancado, mesmo para outros além destes.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 “O rei do sul será forte. Um de seus príncipes se tornará mais forte que ele e terá domínio. Seu domínio será um grande domínio.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 No final dos anos eles se unirão; e a filha do rei do sul virá ao rei do norte para fazer um acordo, mas ela não reterá a força de seu braço. Ele também não ficará de pé, nem seu braço; mas ela será abandonada, com aqueles que a trouxeram, e aquele que se tornou o pai dela, e aquele que a fortaleceu naqueles tempos.
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 “Mas de um tiro de suas raízes um se levantará em seu lugar, que virá para o exército e entrará na fortaleza do rei do norte, e negociará contra eles e prevalecerá.
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 Ele também levará seus deuses com suas imagens fundidas, e com seus bons vasos de prata e de ouro, cativos no Egito. Ele se absterá alguns anos do rei do norte.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 Ele entrará no reino do rei do sul, mas voltará para sua própria terra.
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 Seus filhos farão a guerra e reunirão uma multidão de grandes forças que virão, transbordarão e passarão por ela. Eles voltarão e travarão a guerra, mesmo para sua fortaleza.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 “O rei do sul ficará comovido com raiva e sairá e lutará com ele, mesmo com o rei do norte. Ele enviará uma grande multidão, e a multidão será entregue em suas mãos”.
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 A multidão será transportada, e seu coração será exaltado. Ele derrubará dezenas de milhares, mas não prevalecerá.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 O rei do norte voltará, e enviará uma multidão maior do que a primeira. Ele virá no final dos tempos, mesmo dos anos, com um grande exército e com abundantes provisões.
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 “Naqueles tempos, muitos se levantarão contra o rei do sul. Também os filhos dos violentos entre seu povo se levantarão para estabelecer a visão, mas eles cairão.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 Assim, o rei do norte virá e levantará um monte, e tomará uma cidade bem fortificada. As forças do sul não ficarão de pé, nem suas seletas tropas, nem haverá forças para ficar de pé.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 Mas aquele que vier contra ele fará de acordo com sua própria vontade, e ninguém se levantará diante dele. Ele permanecerá na terra gloriosa, e a destruição estará em suas mãos.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 Ele colocará seu rosto para vir com a força de todo seu reino, e com ele condições eqüitativas. Ele as realizará. Ele lhe dará a filha das mulheres, para destruir o reino, mas ela não ficará de pé, e não será para ele.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 After isto ele voltará seu rosto para as ilhas, e levará muitas, mas um príncipe fará cessar a reprovação oferecida por ele. Sim, além disso, ele fará com que sua reprovação se vire contra ele.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 então ele voltará seu rosto para as fortalezas de sua própria terra; mas ele tropeçará e cairá, e não será encontrado.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 “Então aquele que fizer passar um cobrador de impostos pelo reino para manter sua glória se levantará em seu lugar; mas dentro de poucos dias ele será destruído, não com raiva e não em batalha.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 “Em seu lugar, uma pessoa desprezível se levantará, a quem não tinham dado a honra do reino; mas ele virá em tempo de segurança, e obterá o reino por lisonjas.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 As forças esmagadoras serão esmagadas de diante dele, e serão quebradas. Sim, também o príncipe do pacto.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 Após o tratado feito com ele, ele trabalhará de forma enganosa; pois ele subirá e se tornará forte com poucas pessoas.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 Em tempo de segurança, ele virá mesmo nos lugares mais gordos da província. Ele fará aquilo que seus pais não fizeram, nem os pais de seus pais. Ele espalhará entre eles a presa, o saque e a riqueza. Sim, ele planejará seus planos contra as fortalezas, mas apenas por um tempo.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 “Ele agitará seu poder e sua coragem contra o rei do sul com um grande exército; e o rei do sul travará guerra em batalha com um exército extremamente grande e poderoso, mas ele não vai ficar de pé; pois eles vão inventar planos contra ele.
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 Yes, aqueles que comerem de suas iguarias o destruirão, e seu exército será varrido. Muitos cairão mortos.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 Quanto a estes dois reis, seus corações farão o mal, e falarão mentiras em uma mesa; mas não prosperará, pois o fim ainda será no tempo designado.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 Então ele retornará à sua terra com grande riqueza. Seu coração será contra o santo pacto. Ele tomará medidas e retornará à sua própria terra.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 “Ele voltará na hora marcada e virá para o sul; mas não será na última vez como foi na primeira.
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 Para os navios do Kittim virá contra ele. Portanto, ele ficará de luto, e voltará, e terá indignação contra o santo pacto, e tomará medidas. Ele retornará até mesmo, e terá consideração por aqueles que abandonarem o santo pacto.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 “Forças dele profanarão o santuário, até mesmo a fortaleza, e tirarão a oferta queimada contínua. Em seguida, estabelecerão a abominação que torna desolador.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 Ele corromperá aqueles que fazem maldades contra o pacto por lisonjas; mas as pessoas que conhecem seu Deus serão fortes e tomarão medidas.
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 “Aqueles que são sábios entre o povo instruirão muitos; no entanto, cairão pela espada e pela chama, pelo cativeiro e pela pilhagem, por muitos dias.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 Agora, quando caírem, serão ajudados com uma pequena ajuda; mas muitos se unirão a eles com lisonjas.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 Alguns dos sábios cairão - para refiná-los, purificá-los e torná-los brancos, mesmo até o fim, porque ainda é para o tempo designado.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 “O rei fará de acordo com sua vontade. Ele se exaltará e se engrandecerá acima de todo deus, e falará coisas maravilhosas contra o Deus dos deuses”. Ele prosperará até que a indignação seja consumada, pois o que for determinado será feito.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 Ele não considerará os deuses de seus pais, nem o desejo das mulheres, nem considerará qualquer deus; pois ele se engrandecerá acima de tudo.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 Mas em seu lugar, ele honrará o deus das fortalezas. Ele honrará um deus que seus pais não conheciam com ouro, prata, e com pedras preciosas e coisas agradáveis.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 Ele lidará com as fortalezas mais fortes com a ajuda de um deus estrangeiro. Ele aumentará com glória quem quer que o reconheça. Ele fará com que eles governem sobre muitos, e dividirá a terra por um preço.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 “No momento do fim o rei do sul lutará com ele; e o rei do norte virá contra ele como um redemoinho, com carros, com cavaleiros e com muitos navios. Ele entrará nos países, e transbordará e passará por eles.
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 Ele entrará também na terra gloriosa, e muitos países serão derrubados; mas estes serão libertados de suas mãos: Edom, Moab, e o chefe dos filhos de Ammon.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 Ele também estenderá sua mão sobre os países. A terra do Egito não escapará.
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 Mas ele terá poder sobre os tesouros de ouro e de prata, e sobre todas as coisas preciosas do Egito. Os líbios e os etíopes seguirão seus passos.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 Mas notícias do leste e do norte o incomodarão; e ele sairá com grande fúria para destruir e varrer completamente muitos.
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 Ele plantará as tendas de seu palácio entre o mar e a gloriosa montanha sagrada; no entanto, ele chegará ao seu fim, e ninguém o ajudará.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.

< Daniel 11 >