< 2 Reis 11 >
1 Agora, quando Ataliah, mãe de Acazias, viu que seu filho estava morto, levantou-se e destruiu toda a descendência real.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Mas Jeoseba, filha do rei Jorão, irmã de Acazias, levou Joás, filho de Acazias, e o roubou do meio dos filhos do rei que foram mortos, até mesmo ele e sua enfermeira, e os colocou no quarto; e o esconderam de Atalia, para que ele não fosse morto.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 Ele esteve com ela escondido na casa de Iavé seis anos, enquanto Atalia reinou sobre a terra.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 No sétimo ano Jehoiada mandou buscar e trazer os capitães sobre centenas de caritas e da guarda, e os trouxe até ele na casa de Iavé; e fez um pacto com eles, e fez um pacto com eles na casa de Iavé, e mostrou-lhes o filho do rei.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 Ele lhes ordenou, dizendo: “Isto é o que vocês devem fazer: um terço de vocês, que entram no sábado, serão guardas da guarda da casa do rei;
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 um terço de vocês estará no portão Sur; e um terço de vocês no portão atrás da guarda. Portanto, guardareis a guarda da casa e sereis uma barreira.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 As duas empresas de vocês, mesmo todos os que saírem no sábado, vigiarão a casa de Yahweh ao redor do rei.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 Cercareis o rei, cada homem com suas armas na mão; e aquele que entrar nas fileiras, deixai-o ser morto. Esteja com o rei quando ele sair, e quando ele entrar”.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Os capitães de mais de centenas fizeram de acordo com tudo o que Jehoiada, o sacerdote, ordenou; e cada um deles levou seus homens, aqueles que deveriam entrar no sábado com aqueles que deveriam sair no sábado, e vieram a Jehoiada, o sacerdote.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 O sacerdote entregou aos capitães mais de centenas de lanças e escudos que haviam sido do rei David, que estavam na casa de Yahweh.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 O guarda ficou de pé, cada homem com suas armas na mão, do lado direito da casa para o lado esquerdo da casa, junto ao altar e à casa, ao redor do rei.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Então ele trouxe o filho do rei, colocou a coroa sobre ele e lhe deu o pacto; fizeram-no rei e o ungiram; bateram palmas, e disseram: “Viva o rei!
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Quando Atalia ouviu o barulho da guarda e do povo, veio ao povo na casa de Iavé;
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 e olhou, e eis que o rei estava junto ao pilar, como era tradição, com os capitães e as trombetas do rei; e todo o povo da terra se alegrou, e tocou trombetas. Então Athaliah rasgou suas roupas e gritou: “Traição! Traição!”.
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Jehoiada o padre comandou os capitães de centenas que estavam no exército, e disse-lhes: “Tragam-na para fora das fileiras”. Matem qualquer um que a siga com a espada”. Pois o padre disse: “Não a deixem ser assassinada na casa de Yahweh”.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 Então eles a apreenderam; e ela foi pelo caminho da entrada dos cavalos na casa do rei, e ela foi morta lá.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Jehoiada fez um pacto entre Javé e o rei e o povo, de que eles deveriam ser o povo de Javé; também entre o rei e o povo.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Todo o povo da terra foi para a casa de Baal, e a quebrou. Eles quebraram seus altares e suas imagens completamente em pedaços, e mataram Mattan, o sacerdote de Baal, antes dos altares. O padre nomeou oficiais sobre a casa de Yahweh.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 Ele tomou os capitães por centenas, e os caritas, e a guarda, e todo o povo da terra; e eles derrubaram o rei da casa de Javé, e vieram pelo caminho do portão da guarda até a casa do rei. Ele se sentou no trono dos reis.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 Então todo o povo da terra se alegrou, e a cidade ficou quieta. Eles tinham matado Ataliah com a espada na casa do rei.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Jehoash tinha sete anos de idade quando ele começou a reinar.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.