< 2 Crônicas 25 >

1 Amaziah tinha vinte e cinco anos de idade quando começou a reinar, e reinou vinte e nove anos em Jerusalém. O nome de sua mãe era Jehoaddan, de Jerusalém.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Ele fez o que era certo aos olhos de Iavé, mas não com um coração perfeito.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Agora, quando o reino foi estabelecido para ele, ele matou seus servos que haviam matado seu pai, o rei.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Mas ele não matou seus filhos, mas fez de acordo com o que está escrito na lei no livro de Moisés, como Javé ordenou, dizendo: “Os pais não morrerão pelos filhos, nem os filhos morrerão pelos pais; mas cada homem morrerá por seu próprio pecado”.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Moreover Amaziah reuniu Judah e os ordenou de acordo com as casas de seus pais, sob capitães de milhares e capitães de centenas, até mesmo todos os Judah e Benjamin. Ele os contou de vinte anos para cima, e descobriu que havia trezentos mil homens escolhidos, capazes de sair para a guerra, que podiam manejar lança e escudo.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Ele também contratou cem mil homens poderosos de valor fora de Israel por cem talentos de prata.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Um homem de Deus veio a ele, dizendo: “Ó rei, não deixe o exército de Israel ir com você, pois Javé não está com Israel, com todos os filhos de Efraim”.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Mas se você for, aja, e seja forte para a batalha. Deus vos derrubará diante do inimigo; pois Deus tem poder para ajudar, e para derrubar”.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Amaziah disse ao homem de Deus: “Mas o que devemos fazer pelos cem talentos que eu dei ao exército de Israel? O homem de Deus respondeu: “Yahweh é capaz de lhe dar muito mais do que isso”.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Então o Amaziah os separou, o exército que tinha vindo até ele de Efraim, para voltar para casa novamente. Portanto, a raiva deles foi muito acesa contra Judá, e eles voltaram para casa em fúria.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Amaziah tomou coragem, conduziu seu povo e foi para o Vale do Sal, e atingiu dez mil das crianças de Seir.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 As crianças de Judá levaram dez mil vivos, e os levaram ao topo da rocha, e os jogaram para baixo do topo da rocha, de modo que todos eles foram quebrados em pedaços.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Mas os homens do exército que Amazonas enviou de volta, para que não fossem com ele para a batalha, caíram sobre as cidades de Judá desde Samaria até Beth Horon, e atingiram deles três mil, e levaram muitos saques.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Agora, depois que Amazonas veio do massacre dos edomitas, ele trouxe os deuses dos filhos de Seir, e os colocou para serem seus deuses, e se curvou diante deles e queimou incenso para eles.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Portanto, a ira de Javé ardia contra o Amazias, e ele lhe enviou um profeta que lhe disse: “Por que você procurou os deuses do povo, que não livraram seu próprio povo de suas mãos?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Ao falar com ele, o rei lhe disse: “Fizemos de você um dos conselheiros do rei? Pare! Por que você deveria ser derrubado”? Então o profeta parou e disse: “Eu sei que Deus determinou destruir você, porque você fez isso e não ouviu meus conselhos”.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Então Amaziah, rei de Judá, consultou seus conselheiros e enviou a Joás, filho de Jehoahaz, filho de Jeú, rei de Israel, dizendo: “Venha! Olhemos um para o outro no rosto”.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Joás, rei de Israel, enviou ao Amazonas, rei de Judá, dizendo: “O cardo que estava no Líbano foi enviado ao cedro que estava no Líbano, dizendo: 'Dê sua filha a meu filho como esposa'. Então um animal selvagem que estava no Líbano passou e pisoteou o cardo.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Você diz para si mesmo que atingiu Edom; e seu coração o eleva para se vangloriar. Agora fique em casa. Por que você deveria se meter com problemas, que você deveria cair, até mesmo você e Judá com você”?
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Mas o Amazias não quis ouvir; pois era de Deus, para poder entregá-los nas mãos de seus inimigos, pois eles haviam procurado os deuses de Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Então Joás, rei de Israel, subiu, e ele e Amazias, rei de Judá, olharam um para o outro no rosto de Bete-Semes, que pertence a Judá.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Judá foi derrotado por Israel; assim, cada homem fugiu para sua tenda.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Joás, rei de Israel, tomou o Amazonas, rei de Judá, filho de Joás, filho de Jeoacaz, em Bet-Semes, e o levou a Jerusalém, derrubando o muro de Jerusalém desde a porta de Efraim até a porta da esquina, quatrocentos côvados.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 Ele levou todo o ouro e prata, e todos os vasos que foram encontrados na casa de Deus com Obede-Edom, e os tesouros da casa do rei, e os reféns, e voltou para Samaria.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Amaziah, filho de Joás, rei de Judá, viveu durante quinze anos após a morte de Joás, filho de Jehoahaz, rei de Israel.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Agora o resto dos atos do Amazonas, primeiro e último, eis que eles não estão escritos no livro dos reis de Judá e Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Agora, desde o momento em que o Amazias se afastou de seguir Iavé, eles fizeram uma conspiração contra ele em Jerusalém. Ele fugiu para Laquis, mas eles mandaram atrás dele para Laquis e o mataram lá.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 Eles o trouxeram em cavalos e o enterraram com seus pais na Cidade de Judá.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< 2 Crônicas 25 >