< 2 Crônicas 24 >
1 Joash tinha sete anos de idade quando começou a reinar, e reinou quarenta anos em Jerusalém. O nome de sua mãe era Zíbia, de Berseba.
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 Joás fez o que estava certo aos olhos de Iavé todos os dias de Jehoiada, o sacerdote.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 Jehoiada tomou para ele duas esposas, e se tornou pai de filhos e filhas.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 Depois disso, Joash pretendia restaurar a casa de Yahweh.
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 Ele reuniu os sacerdotes e os levitas, e disse-lhes: “Ide às cidades de Judá, e ajuntai dinheiro para reparar a casa de vosso Deus de todo Israel de ano para ano”. Vejam se agilizam este assunto”. No entanto, os levitas não o fizeram de imediato.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 O rei chamou o chefe Jeoiada e lhe disse: “Por que você não exigiu dos levitas que trouxessem o imposto de Moisés, servo de Iavé, e da assembléia de Israel, de Judá e de Jerusalém, para a Tenda do Testemunho”?
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 Pois os filhos de Atalia, aquela mulher malvada, tinham destruído a casa de Deus; e também deram aos Baal todas as coisas dedicadas da casa de Iavé.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 Então o rei comandou, e eles fizeram uma arca, e a colocaram do lado de fora no portão da casa de Yahweh.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 Eles fizeram uma proclamação através de Judá e Jerusalém, para trazer para Iavé o imposto que Moisés, servo de Deus, impôs sobre Israel no deserto.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 Todos os príncipes e todo o povo se regozijaram, e trouxeram e jogaram no peito, até que o encheram.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 Sempre que a arca era levada aos oficiais do rei pela mão dos levitas, e quando eles viam que havia muito dinheiro, o escriba do rei e o oficial do chefe dos sacerdotes vinham e esvaziavam a arca, e a levavam, e a levavam para seu lugar novamente. Assim eles faziam dia após dia, e recolhiam dinheiro em abundância.
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 O rei e Jehoiada deram-no àqueles que faziam o trabalho do serviço da casa de Yahweh. Eles contrataram pedreiros e carpinteiros para restaurar a casa de Iavé, e também aqueles que trabalharam ferro e bronze para reparar a casa de Iavé.
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 Assim, os trabalhadores trabalharam, e o trabalho de reparo foi adiante em suas mãos. Eles montaram a casa de Deus como ela foi projetada, e a fortaleceram.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 Quando terminaram, trouxeram o resto do dinheiro diante do rei e Jehoiada, dos quais foram feitos vasos para a casa de Javé, até mesmo vasos para ministrar e oferecer, incluindo colheres e vasos de ouro e prata. Eles ofereciam holocaustos na casa de Iavé continuamente durante todos os dias de Jehoiada.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 Mas Jehoiada envelheceu e estava cheio de dias, e morreu. Ele tinha cento e trinta anos de idade quando morreu.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 Eles o enterraram na cidade de Davi entre os reis, porque ele tinha feito o bem em Israel, e para com Deus e sua casa.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 Agora após a morte de Jehoiada, os príncipes de Judá vieram e se curvaram diante do rei. Então, o rei os ouviu.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 Eles abandonaram a casa de Javé, o Deus de seus pais, e serviram aos bastões de Asherah e aos ídolos, então a ira veio sobre Judá e Jerusalém por esta sua culpa.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 Mesmo assim ele enviou profetas a eles para trazê-los novamente a Iavé, e eles testemunharam contra eles; mas eles não quiseram ouvir.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 O Espírito de Deus veio sobre Zacarias, filho de Jehoiada, o sacerdote; e ele ficou acima do povo, e disse-lhes: “Deus diz: 'Por que vocês desobedecem aos mandamentos de Javé, para que não possam prosperar? Porque você abandonou Yahweh, ele também o abandonou”.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 Eles conspiraram contra ele, e o apedrejaram com pedras por ordem do rei na corte da casa de Yahweh.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 Assim, Joás, o rei, não se lembrava da bondade que Jehoiada, seu pai, havia feito com ele, mas matou seu filho. Quando ele morreu, ele disse: “Que Javé olhe para ele, e o retribua”.
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 No final do ano, o exército dos sírios se deparou com ele. Eles vieram a Judá e Jerusalém, e destruíram todos os príncipes do povo dentre o povo, e enviaram todos os seus saques ao rei de Damasco.
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 Pois o exército dos sírios veio com uma pequena companhia de homens; e Javé entregou em suas mãos um exército muito grande, porque abandonaram Javé, o Deus de seus pais. Assim, eles executaram o julgamento de Joás.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 Quando se afastaram dele (pois o deixaram gravemente ferido), seus próprios servos conspiraram contra ele pelo sangue dos filhos de Jehoiada, o sacerdote, e o mataram em sua cama, e ele morreu. Eles o enterraram na cidade de Davi, mas não o enterraram nos túmulos dos reis.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Estes são os que conspiraram contra ele: Zabad, o filho de Shimeath, a amonita, e Jehozabad, o filho de Shimrith, a moabita.
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 Agora, a respeito de seus filhos, da grandeza dos fardos que lhe foram impostos e da reconstrução da casa de Deus, eis que eles estão escritos no comentário do livro dos reis. Amaziah, seu filho, reinou em seu lugar.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.