< 1 Samuel 22 >

1 David partiu de lá e fugiu para a caverna de Adullam. Quando seus irmãos e toda a casa de seu pai ouviram isso, foram até lá para ele.
Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
2 Todos os que estavam em perigo, todos os que estavam em débito e todos os que estavam descontentes se reuniram a ele; e ele se tornou capitão sobre eles. Havia com ele cerca de quatrocentos homens.
Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
3 David foi de lá para Mizpeh dos Moab; e disse ao rei dos Moab: “Por favor, deixe meu pai e minha mãe virem até você, até que eu saiba o que Deus fará por mim”.
Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
4 Ele os trouxe diante do rei dos moabitas; e eles viveram com ele todo o tempo que Davi esteve na fortaleza.
Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
5 O profeta Gad disse a David: “Não fique na fortaleza”. Parta, e vá para a terra de Judá”. Então David partiu, e entrou na floresta de Hereth.
Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
6 Saul soube que David foi descoberto, com os homens que estavam com ele. Agora Saul estava sentado em Gibeah, debaixo da tamargueira em Ramah, com sua lança na mão, e todos os seus servos estavam de pé ao seu redor.
Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
7 Saul disse a seus servos que estavam ao seu redor: “Ouçam agora, seus benjamitas! O filho de Jessé dará a todos vocês campos e vinhedos? Ele fará de vocês todos capitães de milhares e capitães de centenas?
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
8 É por isso que todos vocês conspiraram contra mim, e não há ninguém que me revele quando meu filho faz um tratado com o filho de Jessé, e não há nenhum de vocês que tenha pena de mim, ou que me revele que meu filho agitou meu servo contra mim, para ficar à espera, como é hoje”?
Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
9 Então Doeg o edomita, que estava ao lado dos servos de Saul, respondeu e disse: “Eu vi o filho de Jesse chegando a Nob, a Ahimelech o filho de Ahitub.
Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
10 Ele perguntou a Javé por ele, deu-lhe comida e deu-lhe a espada de Golias, o filisteu”.
Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
11 Então o rei enviou para chamar Ahimelech o sacerdote, o filho de Ahitub, e toda a casa de seu pai, os sacerdotes que estavam em Nob; e todos eles vieram para o rei.
Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
12 Saul disse: “Ouvi agora, filho de Ahitub”. Ele respondeu: “Aqui estou eu, meu senhor”.
Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
13 Saul disse-lhe: “Por que conspiraste contra mim, tu e o filho de Jessé, na medida em que lhe deste pão, e uma espada, e pediste a Deus por ele, que se levantasse contra mim, para ficar à espera, como é hoje”?
Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
14 Então Ahimelech respondeu ao rei, e disse: “Quem entre todos os seus servos é tão fiel como Davi, que é genro do rei, capitão de sua guarda corporal, e honrado em sua casa?
Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
15 Comecei hoje a perguntar a Deus por ele? Fique longe de mim! Não deixe o rei imputar nada a seu servo, nem a toda a casa de meu pai; pois seu servo nada sabia de tudo isso, menos ou mais”.
A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
16 O rei disse: “Certamente morrerás, Ahimelech, tu e toda a casa de teu pai”.
Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
17 O rei disse ao guarda que estava de pé sobre ele: “Vira-te e mata os sacerdotes de Javé, porque sua mão também está com Davi, e porque eles sabiam que ele fugiu e não me revelaram”. Mas os servos do rei não estendiam a mão para cair sobre os sacerdotes de Yahweh.
Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
18 O rei disse a Doeg: “Virem-se e ataquem os padres”! Doeg o Edomita virou-se, e atacou os padres, e matou naquele dia oitenta e cinco pessoas que usavam um éfode de linho.
Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
19 Ele atingiu Nob, a cidade dos padres, com o fio da espada - ambos homens e mulheres, crianças e bebês lactantes, e gado, burros e ovelhas, com o fio da espada.
Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
20 Um dos filhos de Ahimelech, o filho de Ahitub, chamado Abiathar, escapou e fugiu atrás de David.
Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
21 Abiathar disse a David que Saul havia matado os sacerdotes de Yahweh.
Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
22 David disse a Abiathar: “Eu sabia naquele dia, quando Doeg, o Edomita, estava lá, que ele certamente diria a Saul. Eu sou responsável pela morte de todas as pessoas da casa de seu pai”.
Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
23 Fique comigo. Não tenha medo, pois aquele que procura minha vida procura a sua vida. Você estará a salvo comigo”.
Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”

< 1 Samuel 22 >