< 1 Crônicas 22 >

1 Então David disse: “Esta é a casa de Deus Javé, e este é o altar de holocausto para Israel”.
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 David deu ordens para reunir os estrangeiros que estavam na terra de Israel; e colocou pedreiros para cortar pedras vestidas para construir a casa de Deus.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 David preparou ferro em abundância para os pregos das portas dos portões e para os acoplamentos, e bronze em abundância sem peso,
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 e cedros sem número, para os sidônios e o povo de Tiro trouxe cedros em abundância para David.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 David disse: “Salomão meu filho é jovem e terno, e a casa que será construída para Iavé deve ser extremamente magnífica, de fama e de glória em todos os países. Por isso, vou me preparar para ela”. Assim, Davi se preparou abundantemente antes de sua morte.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 Então ele chamou por Salomão seu filho, e ordenou-lhe que construísse uma casa para Iavé, o Deus de Israel.
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 David disse a Salomão, seu filho: “Quanto a mim, estava em meu coração construir uma casa em nome de Javé, meu Deus.
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 Mas a palavra de Javé veio a mim, dizendo: 'Vocês derramaram sangue abundantemente e fizeram grandes guerras'. Não construirás uma casa em meu nome, porque derramaste muito sangue sobre a terra à minha vista”.
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 Eis que vos nascerá um filho, que será um homem de paz”. Eu lhe darei descanso de todos os seus inimigos ao redor; pois seu nome será Salomão, e darei paz e sossego a Israel em seus dias.
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 Ele construirá uma casa em meu nome; e ele será meu filho, e eu serei seu pai; e estabelecerei o trono de seu reino sobre Israel para sempre'.
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Agora, meu filho, que Javé esteja contigo e te faça prosperar, e construa a casa de Javé, teu Deus, como ele falou a teu respeito.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 Que Javé te dê discrição e compreensão, e te coloque no comando de Israel, para que possas manter a lei de Javé teu Deus”.
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 Então você prosperará, se observar os estatutos e as ordenanças que Javé deu a Moisés a respeito de Israel. Seja forte e corajoso. Não tenham medo e não fiquem consternados.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 Agora, eis que em minha aflição preparei para a casa de Javé cem mil talentos de ouro, um milhão de talentos de prata, bronze e ferro sem peso; pois está em abundância. Eu também preparei madeira e pedra; e você pode acrescentar a eles.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 Também há com vocês trabalhadores em abundância - cortadores e trabalhadores de pedra e madeira, e todos os tipos de homens que são hábeis em todo tipo de trabalho;
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 do ouro, da prata, do bronze e do ferro, não há número. Levantem-se e façam, e que Yahweh esteja com vocês”.
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 David também ordenou a todos os príncipes de Israel que ajudassem Salomão, seu filho, dizendo:
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 “Não é Javé o seu Deus com você? Ele não lhe deu descanso de todos os lados? Pois ele entregou os habitantes da terra nas minhas mãos; e a terra está subjugada diante de Iavé e diante de seu povo.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Agora ponha seu coração e sua alma para seguir Yahweh seu Deus. Levantai-vos, pois, e construí o santuário de Javé Deus, para trazer a arca da aliança de Javé e os vasos sagrados de Deus para a casa que será construída em nome de Javé”.
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Crônicas 22 >