< Salmos 96 >

1 Cantai ao SENHOR uma nova canção; cantai ao SENHOR toda a terra.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Cantai ao SENHOR, bendizei ao seu nome; anunciai todos os dias sua salvação.
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Contai sua glória por entre as nações, [e] suas maravilhas por entre todos os povos.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 Porque o SENHOR é grande e muito digno de louvor; ele é mais temível que todos os deuses.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Porque todos os deuses dos povos são ídolos, porém o SENHOR fez os céus;
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Majestade e glória há diante dele; força e beleza [há] em seu santuário.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Reconhecei ao SENHOR, ó famílias dos povos; reconhecei que ao SENHOR pertence a glória e a força.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Reconhecei ao SENHOR a glória de seu nome; trazei ofertas, e entrai nos pátios dele.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Adorai ao SENHOR na glória da santidade; temei perante sua presença toda a terra.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Dizei entre as nações: O SENHOR reina; o mundo está firme, e não se abalará; ele julgará aos povos de forma correta.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Alegrem-se os céus, e enchei de alegria a terra; faça barulho o mar e sua plenitude.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 Saltem contentes o campo e tudo que nele há, e que todas as árvores dos bosque cantem de alegria,
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 Diante do SENHOR; porque ele vem; porque ele vem para julgar a terra. Ele julgará ao mundo com justiça, e aos povos com sua verdade.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.

< Salmos 96 >