< Salmos 94 >

1 Ó Deus das vinganças, SENHOR Deus das vinganças, mostra-te com teu brilho!
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Exalta-te, ó Juiz da terra! Retribui com punição aos arrogantes.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Até quando os perversos, SENHOR, até quando os perversos se alegrarão?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 Eles falam [demais], e dizem palavras soberbas; todos os que praticam a maldade se orgulham.
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Eles despedaçam ao teu povo, SENHOR, e humilham a tua herança.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Eles matam a viúva e o estrangeiro, e tiram a vida dos órfãos.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 E dizem: O SENHOR não vê [isso], e o Deus de Jacó não está prestando atenção.
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Entendei, ó tolos dentre o povo; e vós [que sois] loucos, quando sereis sábios?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Por acaso aquele que criou os ouvidos não ouviria? Aquele que formou os olhos não veria?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Aquele que disciplina as nações não castigaria? É ele o que ensina o conhecimento ao homem.
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 O SENHOR conhece os pensamentos do homem, que são inúteis.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Bem-aventurado é o homem a quem tu disciplinas, SENHOR, e em tua Lei o ensinas;
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 Para tu lhe dares descanso dos dias de aflição, até que seja cavada a cova para o perverso.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Pois o SENHOR não abandonará o seu povo, nem desamparará a sua herança.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Porque o juízo restaurará a justiça, e todos os corretos de coração o seguirão.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Quem se levantará em meu favor contra os malfeitores? Quem se porá em meu favor contra os praticantes de perversidade?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Se o SENHOR não tivesse sido meu socorro, minha alma logo teria vindo a morar no silêncio [da morte].
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Quando eu dizia: Meu pé está escorregando; Tua bondade, ó SENHOR, me sustentava.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Quando minhas preocupações se multiplicavam dentro de mim, teus consolos confortaram a minha alma.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Por acaso teria comunhão contigo o trono da maldade, que faz leis opressivas?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Muitos se juntam contra a alma do justo, e condenam o sangue inocente.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Mas o SENHOR é meu alto retiro, e meu Deus a rocha de meu refúgio.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 E ele fará voltar sobre eles suas próprias perversidades, e por suas maldades ele os destruirá; o SENHOR nosso Deus os destruirá.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Salmos 94 >