< Salmos 84 >
1 Para o regente, com “Gitite”. Salmo dos filhos de Coré: Quão agradáveis são tuas moradas, SENHOR dos exércitos!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
2 Minha alma está desejosa, ao ponto de desmaiar, pelos pátios do SENHOR; meu coração e minha carne clamam ao Deus vivente.
Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
3 Até o pardal acha casa, e a andorinha ninho para si, onde ponha filhotes perto de teus altares, ó SENHOR dos exércitos, Rei meu e Deus meu.
Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
4 Bem-aventurados os que habitam em tua casa; eles louvam a ti continuamente. (Selá)
Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
5 Bem-aventurados aqueles cuja força está em ti, em cujos corações estão os caminhos [corretos].
Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
6 Eles, ao passarem pelo Vale de Baca, fazem dele uma fonte; e a chuva o cobre de bênçãos.
Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
7 Eles vão de força em força; [cada um deles] comparece diante de Deus em Sião.
Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
8 SENHOR Deus dos exércitos, escuta minha oração; inclina os teus ouvidos, ó Deus de Jacó. (Selá)
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
9 Olha o nosso escudo, ó Deus; e observa o rosto do teu ungido.
Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
10 Porque melhor é um dia nos teus pátios, do que mil [fora]. Prefiro estar à porta da casa do meu Deus, a morar nas tendas dos perversos.
Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
11 Porque o SENHOR Deus é sol e escudo; o SENHOR concederá graça e honra; ele não negará o bem aos que andam em integridade.
Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
12 Ó SENHOR dos exércitos, bem-aventurado é o homem que confia em ti!
Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.