< Salmos 73 >
1 Salmo de Asafe: Sim, certamente Deus [é] bom para Israel, para os limpos de coração.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 Eu porém, quase que meus pés se desviaram; quase nada [faltou] para meus passos escorregarem.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Porque eu tinha inveja dos arrogantes, quando via a prosperidade dos perversos.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 Porque não há problemas para eles até sua morte, e o vigor deles continua firme.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Não são tão oprimidos como o homem comum, nem são afligidos como os outros homens;
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Por isso eles são rodeados de arrogância como um colar; estão cobertos de violência como [se fosse] um vestido.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Seus olhos incham de gordura; são excessivos os desejos do coração deles.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Eles são escarnecedores e oprimem falando mal e falando arrogantemente.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 Elevam suas bocas ao céu, e suas línguas andam na terra.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Por isso seu povo volta para cá, e as águas lhes são espremidas por completo.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 E dizem: Como Deus saberia? Será que o Altíssimo tem conhecimento [disto]?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Eis que estes [são] perversos, sempre estão confortáveis e aumentam seus bens.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 [Cheguei a pensar]: Certamente purifiquei meu coração e lavei minhas mãos na inocência inutilmente,
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 Porque sou afligido o dia todo, e castigado toda manhã.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 Se eu tivesse dito [isto], eu falaria dessa maneira; eis que teria decepcionado a geração de teus filhos.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 Quando tentei entender, isto me pareceu trabalhoso.
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Até que entrei nos santuários de Deus, [e] entendi o fim de tais pessoas.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Certamente tu os fazes escorregarem, [e] os lança em assolações.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 Como eles foram assolados tão repentinamente! Eles se acabaram, [e] se consumiram de medo.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Como o sonho depois de acordar, ó Senhor, quando tu acordares desprezarás a aparência deles;
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 Porque meu coração tem se amargurado, e meus rins têm sentido dolorosas picadas.
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 Então me comportei como tolo, e nada sabia; tornei-me como um animal para contigo.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Porém [agora estarei] continuamente contigo; tu tens segurado minha mão direita.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Tu me guiarás com teu conselho, e depois me receberás [em] glória.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 A quem tenho no céu [além de ti]? E [quando estou] contigo, nada há na terra que eu deseje.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Minha carne e meu coração desfalecem; [porém] Deus [será] a rocha do meu coração e minha porção para sempre.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Porque eis que os que ficaram longe de ti perecerão; tu destróis todo infiel a ti.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 Mas [quanto] a mim, bom me é me aproximar de Deus; ponho minha confiança no Senhor DEUS, para que eu conte todas as tuas obras.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.