< Salmos 72 >
1 Para SalomãoDeus, dá teus juízos ao rei, e tua justiça ao filho do rei.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Ele julgará a teu povo com justiça, e a teus aflitos com juízo.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Os montes trarão paz ao povo, e os morros [trarão] justiça.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Ele julgará os pobres do povo, livrará os filhos do necessitado, e quebrará o opressor.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Temerão a ti enquanto durarem o sol e a luz, geração após geração.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Ele descerá como chuva sobre a [erva] cortada, como as chuvas que regam a terra.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Em seus dias o justo florescerá, e [haverá] abundância de paz, até que não [haja] mais a lua.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 E ele terá domínio de mar a mar; e desde o rio até os limites da terra.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Os moradores dos desertos se inclinarão perante sua presença, e seus inimigos lamberão o pó da terra.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Os reis de Társis e das ilhas trarão presentes; os reis de Sabá e Seba apresentarão bens.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 E todos os reis se inclinarão a ele; todas as nações o servirão;
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Porque ele livrará ao necessitado que clamar, e também ao aflito que não tem quem o ajude.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Ele será piedoso para o pobre e necessitado, e salvará as almas dos necessitados.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Ele livrará suas almas da falsidade e da violência, e o sangue deles lhe será precioso.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 E ele viverá; e lhe darão ouro de Sabá, e continuamente orarão por ele; o dia todo o bendirão.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Haverá bastante trigo na terra sobre os cumes dos montes; seu fruto brotará como o Líbano; e desde a cidade florescerão como a erva da terra.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Seu nome permanecerá para sempre; enquanto o sol durar, seu nome continuará; e se bendirão nele; todas as nações o chamarão de bem-aventurado.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Bendito [seja] o SENHOR Deus, o Deus de Israel! Somente ele faz [tais] maravilhas!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 E bendito seja seu glorioso nome eternamente; e que sua glória encha toda a terra! Amem, e amém!
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 [Aqui] terminam as orações de Davi, filho de Jessé.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.